Zuwan Tinubu Faris: Najeriya ta Kulla Yarjejeniyar Ma’adanai da Faransa

Najeriya da Faransa sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwa don inganta ma’adanai masu muhimmanci, musamman tagulla. Yarjejeniyar ta shafi bincike, horo, da musayar dalibai domin inganta fasaha da kwarewa a fannin ma’adanai.

Ana fatan za a rage illar da hakar ma’adanai ke yi wa muhalli da kuma gyara ramuka da aka bari a Najeriya.
 
Yarjejeniyar ta kunshi inganta amfani da ma’adanai kamar tagulla ta hanyar fasahar makamashi mai tsafta.

Ministan ma’adanai, Dr. Dele Alake, wanda ya sanya hannu a madadin Najeriya, ya bayyana cewa wannan mataki zai kawo ci gaba mai dorewa a fannin ma’adanai. Yarjejeniyar ta haɗa da:

Za a horas da dalibai a fannin ma’adanai, tare da gudanar da taron karawa juna sani akai-akai domin inganta kwarewar ma’aikata.

Dr. Alake ya bayyana wannan yarjejeniya a matsayin babbar dama ga gwamnatin Tinubu don kara wa Najeriya daraja a duniya. Hakanan, ana sa ran yarjejeniyar za ta inganta yawan ma’adanai da za a samar, tare da tabbatar da cewa ana gudanar da duk wani aiki a fannin bisa ka’idojin kasa da kasa.

Wannan yarjejeniyar na da muhimmanci wajen tabbatar da ingantaccen tsarin hakar ma’adanai a Najeriya, da kuma samar da sabbin hanyoyin kasuwanci tsakanin Najeriya da Faransa. Ana fatan wannan hadin gwiwa zai kawo ci gaba mai ma’ana ga fannin ma’adinai a ƙasar.