
An gano cewa gwamnonin Najeriya suna ƙoƙarin hana aiwatar da hukuncin da ya ba kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai da kuɗinsu kai tsaye. A wani taro da suka gudanar da shugaban ƙasa Bola Tinubu, gwamnoni sun nuna rashin amincewa da tsarin tura kuɗi kai tsaye daga gwamnatin tarayya zuwa asusun kananan hukumomi ta hanyar CBN.
Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnoni sun nemi a rika tura kuɗi zuwa bankunan kasuwanci maimakon CBN, wanda ke ƙarƙashin hukuma. Wannan mataki yana nufin cewa suna son a dakatar da tsarin har sai an biya basussukan da ake bin kananan hukumomi.
A ranar 11 ga Yuli, kotun koli ta yanke hukuncin cewa ya zama dole a rika biyan kuɗin kananan hukumomi kai tsaye, wanda hakan ya jawo cece-kuce a tsakanin gwamnonin. Alkalai sun bayyana cewa gwamnoni ba za su iya rike kuɗin kananan hukumomi ko nada shugabanni ba tare da zabe ba.
Gwamnonin sun bayyana damuwarsu kan ikon da CBN ke da shi wajen gudanar da kuɗaɗen kananan hukumomi. Sun bayyana cewa idan CBN ke rike da kuɗin, ana buƙatar amincewar akanta janar na ƙasa kafin a fitar da su.
A halin yanzu, gwamnonin na ci gaba da tattaunawa da gwamnatin tarayya domin samun mafita kan batun bai wa kananan hukumomi ‘yanci da kuma yadda za a tsara al’amuran kuɗinsu. Wannan shiri na gwamnonin na nufin tabbatar da cewa suna da iko kan harkokin kuɗin kananan hukumomi a jihohinsu.