Siyasa

Gwamna Ya Gaza Hakuri, Ya Kafa Kwamitin Binciken Tsohon Gwamnan Jiharsa

Gwamna Ya Gaza Hakuri, Ya Kafa Kwamitin Binciken Tsohon Gwamnan Jiharsa

Siyasa
Kwanaki 12 kacal bayan hawa kujerar gwamna, Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo ya kafa kwamitin binciken tsohuwar gwamnatin jihar da ta sauka. Wannan mataki da gwamnan ya dauka ya janyo cece-kuce a fadin jihar, inda wasu ke ganin shi ne abin da ya dace yayin da wasu ke ganin ba lokaci bane da ya dace da fara binciken tsohon gwamna. Kwamitin binciken, wanda ya kunshi mutane 14, zai binciki zargin badakalar da aka yi a gwamnatin tsohon Gwamna Godwin Obaseki, ciki har da zargin karkatar da kudaden gwamnati da kuma kwashe motocin gwamnati. Ana sa ran kwamitin zai kammala binciken sa cikin watanni uku. Gwamna Okpebholo ya ce ya kafa kwamitin ne domin ya yi adalci ga al'ummar jihar Edo. Ya ce ba zai bari a ci amanar jama'a ba. Ya kuma ce binciken zai taimaka wajen gano gaskiya game da za...
Ana Zargin Alaka Ta Yi Tsami Tsakanin Namadi da Badaru, Gwamna Ya Magantu

Ana Zargin Alaka Ta Yi Tsami Tsakanin Namadi da Badaru, Gwamna Ya Magantu

Siyasa
Ana zargin akwai baraka a jam'iyyar APC da ke jihar Jigawa tsakanin tsohon gwamnan jihar, Badaru Abubakar da Gwamna Umar Namadi. Wani rahoton Vanguard ya ce lamarin ya faro ne tun lokacin kaddamar da yan Majalisa a jihar da zaben kakakinta a watan Yunin 2023. Yayin wata ganawa, an amince za a zabi Idris Garba kakakin Majalisar wanda daga bisani gwamnan ya sauya ra'ayi inda ya goyi bayan Haruna Dangyatin wanda bai yiwa masoyan Badaru dadi ba. Daga bisani an yi kokarin tsige kakakin Majalisar wanda ya sha da kyar, a kokarin daukar fansa a wancan lokaci inda Dangyatin ya dakatar da wasu ciyamomi da ake ganin yaran Badaru ne kan zargin badakala. Bayan fashewar tankar mai da ta yi ajalin mutane da dama a karamar hukumar Taura, Badaru ya tura tawaga inda ya ba da gudunmawar N20m ba t...
Gwamnonin PDP sun Shiga Ganawa a Jos, Sun Jero Tsare-Tsaren Kawo Sauyi a Kasa

Gwamnonin PDP sun Shiga Ganawa a Jos, Sun Jero Tsare-Tsaren Kawo Sauyi a Kasa

Siyasa
Gwamnonin jam'iyyar PDP sun shiga ganawa ta musamman a jihar Plateau domin tattauna matsalolin da jam'iyyar ke fuskanta da kuma jero tsare-tsaren kawo sauyi a kasar nan. Mai masaukin baki, Gwamna Caleb Mutfwang ya tabbatar da himmatuwarsu wurin kawo hadin kai a jam'iyyar, cewar Leadership. Ya kuma ba da tabbacin dawo da martabar jam'iyyar a idon yan Najeriya kamar yadda take. Gwamna Mutfwang ya godewa gwamnonin PDP da kuma masu ruwa da tsakin jam'iyyar da suka cika a jihar domin wannan taro. Duk da wannan taro musamman an shirya ne domin gwamnoni, amma abin farin ciki ne yadda jiga-jigan jam'iyyar suka cika wannan taro domin ba gwamnonin goyon baya." Jam'iyyar PDP ba iya zakulo hanyoyin kawo zaman lafiya a cikinta za ta yi ba har da dawo da martabar jam'iyyar a idon yan Naje...
An Kaure da Fada da Akpabio a Majalisa kan Fifita Sanatocin Arewa? Gaskiya Ta Fito

An Kaure da Fada da Akpabio a Majalisa kan Fifita Sanatocin Arewa? Gaskiya Ta Fito

Siyasa
An Kaure da Fada da Akpabio a Majalisa kan Fifita Sanatocin Arewa? Gaskiya Ta Fito An yi ta yada jita-jita cewa an kaure da fada tsakanin shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Sanata Opeyemi Bamidele a ranar Laraba, 20 ga watan Nuwamba, 2024. Wani mai amfani da kafar X, Jackson Ude, ya wallafa cewa Bamidele ya zargi Akpabio da nuna wariya ga Sanatocin Kudu wurin ba da shugabancin manyan kwamitoci. Ude ya ce Bamidele ya ce Akpabio na ba da manyan kwamitoci ga abokansa da ke Arewacin Najeriya inda da yake fifita su fiye da sanatocin Kudu. Sai dai Sanata Bamidele ya yi watsi da lamarin a shafin Facebook inda ya ce wanda ya yada labarin ya saba batawa mutane suna. Sanarwar ta ce babu gaskiya kan rigima tsakanin Akpabio da Sanata Bamidele a ranar Laraba, 20 ga watan Nuw...
Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Jita-jitar Hana Kudade ga jihar Rivers

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Jita-jitar Hana Kudade ga jihar Rivers

Labarai, Siyasa
Gwamnatin tarayya ta karyata rahotannin da ke yawo cewa ta hana jihar Rivers kuɗaɗe daga asusunta duk wata. A cewar daraktan yaɗa labarai na ofishin akanta janar na tarayya, Mista Bawa Mokwa, har yanzu ana ci gaba da bayar da kuɗaɗen na watan Oktoba waɗanda asusun gwamnatin tarayya ke rabawa jihohi da ƙananan hukumomi.Mokwa ya bayyana cewa jihar Rivers za ta samu na ta kuɗaɗen saboda ɗaukaka ƙarar da aka yi kan hukuncin kotun da ya hana a ba ta kuɗaɗe duk wata. "Jihar Rivers za ta samu kuɗaɗen saboda ɗaukaka ƙarar da aka yi domin neman a dakatar da aiwatar da hukuncin."A halin da ake ciki kuma, kotun ɗaukaka ƙara dake zamanta a Abuja a ranar Juma’a ta tanadi hukunci a wasu ƙararraki biyar da suka biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya ta yanke kan rikicin siyasar jihar Rivers. Ɗa...
Sanata Ya Nada Hadimai a Bangaren Addinin Musulunci da Kiristanci a kudancin Kaduna

Sanata Ya Nada Hadimai a Bangaren Addinin Musulunci da Kiristanci a kudancin Kaduna

Siyasa
A wani mataki na kara tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kaduna, Sanata Sunday Katung ya nada Malam Ilyasu Musa da Fasto Gideon Mutum a matsayin hadimai na musamman a bangaren addinin Musulunci da Kiristanci. Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Hon Wilson Yangye ya fitar a shafin Facebook a ranar Alhamis, 21 ga watan Nuwamba, 2024. Sanata Katung, wanda ke wakiltar Kaduna ta Kudu a majalisar dattawa, ya nada Malam Ilyasu a bangaren addinin Musulunci yayin da Fasto Mutum zai kula da bangaren Kiristoci. Karin Bayani: An nada Malam Ilyasu ne saboda kwarewarsa a fannin zaman lafiya da kuma kasancewarsa sakataren Jama'atu Nasril Islam (JNI) a Kaduna ta Kudu.Fasto Mutum shi ne ya assasa kungiyoyin zaman lafiya na Amaya Peace Foundation (APF) da We...
Majalisa Ta Ki Amincewa da Kara Wa’adin Shugaban Kasa da Gwamnoni

Majalisa Ta Ki Amincewa da Kara Wa’adin Shugaban Kasa da Gwamnoni

Siyasa
Majalisar wakilan Najeriya ta ki amincewa da kudurin da zai kara wa'adin shugaban kasa da gwamnoni zuwa shekara shida amma wa'adi daya kawai. Wannan shawarar ta zo ne bayan da majalisar ta yi zamanta a ranar Alhamis, 21 ga Nuwamba, 2024. A yayin zaman, yan majalisar sun yi fatali da kudurin. Kudurin da aka yi watsi da shi na nufin zababben shugaban kasa da gwamna da shugabannin kananan hukumomi za su yi mulki sau daya na shekara shida kawai. Dan majalisa daga jihar Imo, Ikeagwuonu Ugochinyere da wasu yan majalisu 33 ne suka bijiro da kudurin a farkon wannan shekarar, da nufin samar da daidaito a tsarin mulkin kasar. Amma a lokacin da aka kira kuri'ar murya a zaman na Alhamis, yan majalisar da suka ce a'a sun shafe muryar wadanda ke bukatar a cigaba da duba kudurin. Wannan na nufin an...
Yan Adawa Sun Fara Wani Shirin Ture Tinubu a Zaɓen 2027

Yan Adawa Sun Fara Wani Shirin Ture Tinubu a Zaɓen 2027

Siyasa
Jam'iyyar Labour, wacce ta samu nasarar shiga sahun manyan jam'iyyun siyasa a Najeriya, ta fara shirin tunkarar zaɓen 2027. Jam'iyyar ta yi wani taro na musamman domin fara shirin kifar da gwamnatin APC a zaɓen shekarar 2027.A yayin taron, wanda aka gudanar a Abuja, babban birnin Najeriya, shugaban tattaro jama'a na jam'iyyar LP, Marcel Ngogbehi ya ce ba za su yi kasa a gwiwa ba har sai sun shiga Aso Rock Villa a 2027.Ngogbehi ya ce jam'iyyar LP za ta mayar da hankali kan neman goyon bayan yan ƙasa a yanzu, domin samun nasara a zaɓen 2027. Ya ce za su hada kan al'umma, domin samun karɓuwa a sassan Najeriya."Mun shirya wannan taron ne domin neman yadda za mu hada kai mu samar da mafita ga matsalolin Najeriya," in ji Ngogbehi. "Ina kira a gare ku da ku kulla alaka da mutane, ku sanar da su m...
An Bukaci Yan Arewa Su Yi Watsi da Kwankwaso Kan Taɓa Tinubu

An Bukaci Yan Arewa Su Yi Watsi da Kwankwaso Kan Taɓa Tinubu

Siyasa
Wata kungiyar magoya bayan shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, NAT ta yi martani ga Sanata Rabi'u Kwankwaso kan sukar kudirin haraji.Kungiyar ta yi kira ga yan Arewa da su yi watsi da maganganun da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi na sukar sauya fasalin harajin Najeriya.A karon farko, madugun Kwankwasiyya ya soki kudirin harajin Shugaba Bola  Ahmad Tinubu ne a wani taron yaye ɗalibai a jami'ar Skyline ta jihar Kano.NAT ta ce Kwankwaso bai kyauta ba da ya soki kudirin harajin a gaban dalibai. Kungiya ta yi raddi ga Kwankwaso kan sukar Tinubu.Vanguard ta wallafa cewa kungiyar ta ce kamata ya yi Kwankwaso ya yi wa daliban bayanin mai kyau a kan dokar harajin maimakon suka." Shugaban kasa Bola Tinubu ya kawo kudirin haraji ne domin tabbatar da cigaba a Najeriya, ciki har da jihohin Arewa. ...