
Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Jita-jitar Hana Kudade ga jihar Rivers
Gwamnatin tarayya ta karyata rahotannin da ke yawo cewa ta hana jihar Rivers kuɗaɗe daga asusunta duk wata. A cewar daraktan yaɗa labarai na ofishin akanta janar na tarayya, Mista Bawa Mokwa, har yanzu ana ci gaba da bayar da kuɗaɗen na watan Oktoba waɗanda asusun gwamnatin tarayya ke rabawa jihohi da ƙananan hukumomi.Mokwa ya bayyana cewa jihar Rivers za ta samu na ta kuɗaɗen saboda ɗaukaka ƙarar da aka yi kan hukuncin kotun da ya hana a ba ta kuɗaɗe duk wata. "Jihar Rivers za ta samu kuɗaɗen saboda ɗaukaka ƙarar da aka yi domin neman a dakatar da aiwatar da hukuncin."A halin da ake ciki kuma, kotun ɗaukaka ƙara dake zamanta a Abuja a ranar Juma’a ta tanadi hukunci a wasu ƙararraki biyar da suka biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya ta yanke kan rikicin siyasar jihar Rivers. Ɗa...