Jam’iyyar Peter Obi ta Fara Shiri a Jihohi 36 domin Kawar da Tinubu a 2027
Jam’iyyar Labour (LP) ta kaddamar da shirin sake tsara tsarin jagorancin jihohi da kuma shirin tunkarar zaɓen 2027, a matsayin wani mataki na karfafa gwiwar jam'iyyar bayan kalubalen da suka fuskanta a zaɓen 2023.
A cikin sanarwar da jam'iyyar ta fitar, an bayyana cewa za a kafa kwamitin jagoranci a jihohi domin ƙarfafa alaƙa tsakanin shugabannin jam'iyyar da kungiyoyin sa-kai. Hakan zai haɗa da horar da sababbin mambobi da kuma shigar da su cikin tsarin jam'iyyar a matakai daban-daban.
Jam’iyyar LP ta ce za ta ƙaddamar da sabon tsarin shugabanci a hedkwatocin jam’iyyar a fadin Najeriya a ranar Juma’a. Wannan tsari yana nufin gina cibiyoyin jagoranci a jihohi da za su haɗa shugabannin gangami da wakilai, tare da ba su horo na musamman don gudanar da ayyukansu cikin nasara.
Hakanan...








