Siyasa

Yan Adawa Sun Fara Wani Shirin Ture Tinubu a Zaɓen 2027

Yan Adawa Sun Fara Wani Shirin Ture Tinubu a Zaɓen 2027

Siyasa
Jam'iyyar Labour, wacce ta samu nasarar shiga sahun manyan jam'iyyun siyasa a Najeriya, ta fara shirin tunkarar zaɓen 2027. Jam'iyyar ta yi wani taro na musamman domin fara shirin kifar da gwamnatin APC a zaɓen shekarar 2027.A yayin taron, wanda aka gudanar a Abuja, babban birnin Najeriya, shugaban tattaro jama'a na jam'iyyar LP, Marcel Ngogbehi ya ce ba za su yi kasa a gwiwa ba har sai sun shiga Aso Rock Villa a 2027.Ngogbehi ya ce jam'iyyar LP za ta mayar da hankali kan neman goyon bayan yan ƙasa a yanzu, domin samun nasara a zaɓen 2027. Ya ce za su hada kan al'umma, domin samun karɓuwa a sassan Najeriya."Mun shirya wannan taron ne domin neman yadda za mu hada kai mu samar da mafita ga matsalolin Najeriya," in ji Ngogbehi. "Ina kira a gare ku da ku kulla alaka da mutane, ku sanar da su m...
An Bukaci Yan Arewa Su Yi Watsi da Kwankwaso Kan Taɓa Tinubu

An Bukaci Yan Arewa Su Yi Watsi da Kwankwaso Kan Taɓa Tinubu

Siyasa
Wata kungiyar magoya bayan shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, NAT ta yi martani ga Sanata Rabi'u Kwankwaso kan sukar kudirin haraji.Kungiyar ta yi kira ga yan Arewa da su yi watsi da maganganun da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi na sukar sauya fasalin harajin Najeriya.A karon farko, madugun Kwankwasiyya ya soki kudirin harajin Shugaba Bola  Ahmad Tinubu ne a wani taron yaye ɗalibai a jami'ar Skyline ta jihar Kano.NAT ta ce Kwankwaso bai kyauta ba da ya soki kudirin harajin a gaban dalibai. Kungiya ta yi raddi ga Kwankwaso kan sukar Tinubu.Vanguard ta wallafa cewa kungiyar ta ce kamata ya yi Kwankwaso ya yi wa daliban bayanin mai kyau a kan dokar harajin maimakon suka." Shugaban kasa Bola Tinubu ya kawo kudirin haraji ne domin tabbatar da cigaba a Najeriya, ciki har da jihohin Arewa. ...