
PDP Ta Ayyana Kujerar ‘Yar Majalisar Tarayya da Ta Koma APC a matsayin Babu Kowa
Jam'iyyar PDP ta ayyana kujerar Hon. Erhiatake Ibori-Suenu a Majalisar Tarayya a matsayin babu kowa, bayan ficewarta daga jam'iyyar zuwa APC. Wannan mataki na PDP ya biyo bayan sanarwar da Ibori-Suenu ta fitar, inda ta bayyana dalilan ficewarta daga PDP saboda rikice-rikicen da ta fuskanta a cikin jam'iyyar.Hon. Erhiatake Ibori-Suenu, wacce ke wakiltar mazabar Ethiope ta Tarayya a jihar Delta, ta sanar da komawarta APC a wata wasika da ta rubutawa shugaban PDP na karamar hukumar Ethiope West. A cikin wasikar, ta bayyana cewa ta yanke wannan shawara ne bisa ga rashin shigar da ita cikin harkokin jam’iyyar a matakin jiha.Jam'iyyar PDP ta bayyana wannan lamari a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin Facebook, inda ta bukaci hukumar INEC da ta gudanar da sabon zaɓe domin cike gurbin kujera...