
Jam’iyyar NNPP Ta Hango Kujerar Gwamnan da Za Ta Iya Ƙwacewa daga Hannun PDP
Jam'iyyar NNPP (New Nigeria Peoples Party) ta bayyana cewa tana da kwarin guiwar za ta kai labari a zaɓen gwamnan jihar Osun da za a yi a shekarar 2026. A cewar jam'iyyar, Gwamna Ademola Adeleke na PDP ya gaza wajen gudanar da mulkin jihar, wanda hakan zai sa mutanen Osun su yi ƙoƙarin canza shi a zaɓen mai zuwa.A lokacin taron kaddamar da ofisoshinta a kananan hukumomin Ila, Boripe, da Ifelodun, shugaban NNPP na jihar Osun, Dr. Tosin Odeyemi, ya bayyana cewa jam'iyyar tana da kyakkyawar dama don samun nasara a zaɓen gwamna a 2026. Ya ce, “Yadda mutane suka dawo daga rakiyar gwamnatin Adeleke da halin matsin da ake ciki a kasa zai taimaka mana wajen samun galaba."Dr. Odeyemi ya ƙara da cewa matsin tattalin arziki da ake fama da shi a yanzu yana da tasiri sosai kan APC da PDP, wanda hakan k...