APC Ta Fice Daga Zaben Kananan Hukumomi a Osun, Ta Bayyana Dalilan Ficewarta
Jam’iyyar APC ta sanar da janyewar ta daga zaben kananan hukumomi da aka shirya yi a jihar Osun ranar 22 ga Fabrairu, 2025. Wannan mataki ya biyo bayan hukuncin kotu da ya mayar da shugabanninta ofisoshinsu, wanda jam’iyyar ta ce ya ba su damar komawa bakin aiki.APC ta bayyana cewa hukuncin kotu ya tabbatar da cewa shugabannin jam’iyyar sun koma ofis, don haka ba za ta shiga zabe ba. Wannan lamari ya janyo rikici tsakanin APC da PDP, wanda ya haifar da asarar rayuka da jikkata wasu mutane a yayin tashin hankali da ya biyo baya.A cikin wasikar da sakataren yada labaranta, Alao Kamorudeen, ya fitar, APC ta bayyana cewa hukuncin Babbar Kotun Tarayya da aka soke a ranar 10 ga Fabrairu ya ba da damar karbar shugabanci. Jam’iyyar ta ce saboda wannan hukunci, kujerun shugabannin ba su sake ba, do...








