Kotu Ta Dakatar da Binciken Sanata Natasha a Majalisar Dattawa
Babbar kotun tarayya a Abuja ta bayar da umarni na wucin gadi wanda ya dakatar da Kwamitin Ladabtarwa na Majalisar Dattawa daga ci gaba da bincikar Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan. Wannan hukunci ya biyo bayan zargin da Sanatar Natasha ta yi wa shugaban majalisar, Godswill Akpabio, na neman yin lalata da ita domin samun fifiko a kan kudurorinta.Kotun ta umarci cewa binciken da ake shirin yi wa Sanata Natasha ya kasance a bude ga kowa da kowa, ba tare da boye-boye ba. Wannan hukunci ya hana kwamitin ci gaba da shirin dakatar da Sanatar har sai an sake duba shari'ar da ke gabanta.Sanata Natasha ta bayyana cewa ta ki amincewa da bukatar Akpabio, wanda hakan ya sa ya yi amfani da wannan wajen fatali da duk wata bukata ta ci gaban yankinta a majalisa. A nasa bangaren, Akpabio ya musanta zargin, ...








