Hasashen Sanata Marafa Kan Kalubalen Tinubu a Zaɓen 2027
Sanata Kabiru Garba Marafa daga jihar Zamfara ya yi gargadi kan makomar Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa zai fuskanci ƙalubale wajen samun goyon bayan 'yan Arewa a zaɓen 2027. Wannan magana ta fito ne a yayin da Marafa ke bayyana damuwarsa game da yadda gwamnatin Tinubu ke watsi da bukatun al'ummar Arewa.Marafa, wanda a baya ya kasance babban mai goyon bayan Tinubu a yakin neman zaɓe na 2023, ya zargi gwamnatin da rashin bayar da muhimmanci ga yankin Arewa. Ya ce akwai barazanar Tinubu zai rasa goyon bayan yawancin 'yan Arewa idan abubuwan da ake gani yanzu ba su canza ba.A cikin jawabin da ya yi, Marafa ya lissafa tabarbarewar tsaro da gaza kammala manyan ayyuka a Arewa a matsayin dalilan da ke haifar da rashin jin daɗin al'umma. Ya ce, "A cikin shekaru biyu, ban ga wani ba...








