Labarai

Gobara Ta Tashi a Asibitin Koyarwa na LAUTECH, Dukiya Mai Yawa Ta Kone

Gobara Ta Tashi a Asibitin Koyarwa na LAUTECH, Dukiya Mai Yawa Ta Kone

Labarai
Wata mummunar gobara ta tashi a asibitin koyarwa na jami'ar Ladoke Akintola (LAUTECH) da ke Ogbomoso a jihar Oyo, yankin Kudu maso Yammacin Najeriya. Gobarar, wacce ta tashi da sanyin safiyar ranar Asabar, 23 ga watan Nuwamba, 2024, ta yi sanadiyyar lalata dukiya mai tarin yawa ta miliyoyin Naira. Gobarar ta shafi sashin kula da ba da agajin gaggawa da hadurra na asibitin, inda ta lalata kayan ofis, littattafai, na'urorin lantarki, rufi da silin. Shaidun gani da ido sun ce gobarar ta auku ne da misalin ƙarfe 5:00 na safe, sakamakon tsartsarin wutar lantarki daga wani ofishi. Hukumomin asibitin sun yi gaggawar fitar da majinyata 16 daga sashin a lokacin da gobarar ta tashi, domin kaucewa asarar rayuka. Jami'in hulɗa da jama'a na asibitin, Omotayo Ogunleye, ya tabbatar da faruwar lamar...
Fusatattun Mutane Sun Bankawa Masu Karbar Kudin Haraji Wuta a Anambra

Fusatattun Mutane Sun Bankawa Masu Karbar Kudin Haraji Wuta a Anambra

Labarai
A wani lamari mai tayar da hankali, wasu fusatattun mutane sun dauki doka a hannunsu a jihar Anambra, inda suka bankawa wasu masu karbar kudin haraji wuta. Wannan lamari ya auku ne bayan masu karbar harajin sun jawo wani mutum ya rasa ransa a kokarin karbar kudi wajen wani direba. An ruwaito cewa lamarin ya auku ne a karshen mako a hanyar tsohuwar kasuwa, kusa da titin Venn a Egerton. Shaidun gani da ido sun bayyana cewa jami'an harajin sun yi kokawa da wani direban babbar mota wajen karbar sitiyarinsa. Direban ya rasa yadda zai yi, lamarin da ya sa motar ta kwace sannan ta bugi wani mutum da ke bakin titi. Fusatattun mutane, wadanda suka hada da masu tuka keke Napep, sun hana jami'an harajin tserewa daga wurin da lamarin ya faru. Sun lakada musu duka da abubuwa daban-daban kafin su ...
Yan Takarar Gwamna a Ondo Sun Nemi Haɗin Kai da Aiyedatiwa Bayan Nasararsa

Yan Takarar Gwamna a Ondo Sun Nemi Haɗin Kai da Aiyedatiwa Bayan Nasararsa

Labarai
Yan takarar gwamna 13 da suka fafata a zaɓen jihar Ondo sun bayyana matsayarsu kan nasarar Gwamna Lucky Aiyedatiwa, inda suka ce sun amince da sakamakon zaɓen kuma suna shirin haɗa kai da shi domin gina sabuwar jihar Ondo. Sun bayyana hakan ne lokacin da suka gana da Aiyedatiwa a ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Akure, babban birnin jihar a ranar Juma'a. 'Yan takarar sun yi alƙawarin goyon bayan gwamnatin Aiyedatiwa domin ci gaban jihar, sannan suka buƙaci ya dama da sauran jam'iyyun siyasar da suka fafata da shi. Jam'iyyun da suka halarci taron sun haɗa da Accord (A), AA, APM, NNPP, APP, ADP, ADC, APGA, LP, YP, YPP, BP da ZLP. Gwamna Aiyedatiwa ya yabawa 'yan takarar da shugabannin jam'iyyunsu kan alƙawarin da suka yi na marawa gwamnatinsa baya, inda ya ce ba zai yi wasa da ...
Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Jita-jitar Hana Kudade ga jihar Rivers

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Jita-jitar Hana Kudade ga jihar Rivers

Labarai, Siyasa
Gwamnatin tarayya ta karyata rahotannin da ke yawo cewa ta hana jihar Rivers kuɗaɗe daga asusunta duk wata. A cewar daraktan yaɗa labarai na ofishin akanta janar na tarayya, Mista Bawa Mokwa, har yanzu ana ci gaba da bayar da kuɗaɗen na watan Oktoba waɗanda asusun gwamnatin tarayya ke rabawa jihohi da ƙananan hukumomi.Mokwa ya bayyana cewa jihar Rivers za ta samu na ta kuɗaɗen saboda ɗaukaka ƙarar da aka yi kan hukuncin kotun da ya hana a ba ta kuɗaɗe duk wata. "Jihar Rivers za ta samu kuɗaɗen saboda ɗaukaka ƙarar da aka yi domin neman a dakatar da aiwatar da hukuncin."A halin da ake ciki kuma, kotun ɗaukaka ƙara dake zamanta a Abuja a ranar Juma’a ta tanadi hukunci a wasu ƙararraki biyar da suka biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya ta yanke kan rikicin siyasar jihar Rivers. Ɗa...
Kano Za Ta Cika Makil da Yan Kasuwa Yayin Bikin Baje Koli karo na 45

Kano Za Ta Cika Makil da Yan Kasuwa Yayin Bikin Baje Koli karo na 45

Labarai
A ranar Asabar, 23 ga watan Nuwamba, 2024, za a bude kasuwar baje koli ta duniya a Kano, inda tuni kamfanoni su ka shirya halartar gagarumin taron. Cibiyar bunkasa ciniki da masana'antu da ma'adinai da ayyukan gona a jihar (KACCIMA), ta bayyana cewa shirye-shirye sun kammala domin tabbatar da taro mai inganci. Ana sa ran kamfanoni daga ciki da wajen Najeriya ne za su hallara a kasuwar domin baje hajarsu ga masu sha'awa. Kamfanonin sun hada da kasar India da na Nijar, yayin da aka tsara cewa kowa zai iya shiga bajekolin kyauta. Shugaban KACCIMA, Garba Imam ya fadi cewa akalla kamfanoni 300 ne aka da tabbacin za su halarci kasuwar baje koli. Ya kara da cewa kamfanonin sun hada da na cikin Najeriya da kasashen waje kamar su India da Nijar. Alhaji Garba Imam ya bayyanacewa za a iya sh...
Rundunar Hisbah Ta Ƙara Faɗaɗuwa a Arewa, Ana Neman Ba Su Cikakken Iko

Rundunar Hisbah Ta Ƙara Faɗaɗuwa a Arewa, Ana Neman Ba Su Cikakken Iko

Labarai
A ranar Alhamis, 22 ga watan Nuwamba, 2024, gwamnatin jihar Sokoto ta kaddamar da sabuwar rundunar Hisbah a jihar. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kira ga a ba rundunar Hisbah cikakken iko a jihohin Arewacin Najeriya.Gwamna Ya Yi Kira Ga Yan Hisbah Da Su Yi Aiki TuƙuruGwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya jagoranci kaddamar da rundunar Hisbah din, inda ya yi kira ga yan Hisbah da su kasance wakilai na gari. Ya ce su yi aiki tuƙuru da kuma kiyaye dokokin kasa yayin mu'amala da al'umma.Gwamna Aliyu ya kuma jaddada cewa yan Hisbah ba kamar yan sanda ba ne, saboda haka idan suka kama mutum su mika shi ga jami'an tsaro. Ya kuma ce gwamnati ta samar da ofisoshi, motoci, da ma'aikata masu nagarta domin tabbatar da nasarar aikin Hisbah a jihar.Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Ba Yan Hisbah ...
Kotun Koli Ta Soke Dokar Caca Ta Kasa, Ta Ce Majalisar Tarayya Ba Ta Da Hurumi

Kotun Koli Ta Soke Dokar Caca Ta Kasa, Ta Ce Majalisar Tarayya Ba Ta Da Hurumi

Labarai
A yau Juma'a, 22 ga watan Nuwamba, 2024, kotun koli ta Najeriya ta soke dokar caca ta kasa ta 2005, inda ta ce majalisar dokokin tarayya ba ta da hurumin yin doka a kan batutuwan da suka shafi caca da wasannin sa'a. Wannan hukuncin ya zo ne bayan karar da jihar Legas da wasu jihohi suka shigar a shekarar 2008, inda suka kalubalanci dokar caca ta kasa, suna masu cewa ta saba wa kundin tsarin mulkin kasar. Kwamitin alkalai bakwai ƙarƙashin jagorancin Mai shari'a Muhammed Idris ne ya yanke wannan hukuncin ranar Juma'a, 22 ga watan Nuwamba A hukuncin da ya karanto a harabar kotun ƙoli, Mai Shari'a Mohammed Idris, ya ba da umarni daina amfani da dokar caca a faɗin jihohi 36 a Najeriya. Ya ce dokar za ta cu gaba aiki ne a babbar birnin tarayya Abuja kaɗai saboda nan ne majalisar dokoki ...
An Shiga Fargaba Bayan Harin Sojoji Kan ‘Yan Ta’adda Ya Hallaka Bayin Allah

An Shiga Fargaba Bayan Harin Sojoji Kan ‘Yan Ta’adda Ya Hallaka Bayin Allah

Labarai
Ana fargaba cewa harin da sojoji suka kai domin fatattakar 'yan ta'adda a jihar Katsina ya salwantar da rayukan fararen hula. An ruwaito cewa mutane da dama sun kwanta dama, yayin da wasu da yawa suka samu munanan raunuka.Harin da sojojin sama suka kai a kauyen Shuwa da ke karamar hukumar Faskari ya jawo cece-kuce, inda wasu ke zargin cewa an kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba. Gwamnatin jihar Katsina ta musanta wannan zargi, inda ta ce sojojin sun kai harin ne bayan sun tabbatar da cewa 'yan ta'adda ne a wurin.Rahotanni sun nuna cewa harin ya janyo asarar rayuka da dama, ciki har da mata da kananan yara. Wani mazaunin kauyen Shuwa ya shaida cewa: "Sojojin sun jefa bam ne a kanmu, ba tare da sun san ko mu 'yan ta'adda ne ko ba mu ba. Mun rasa mutane da dama, ciki har da 'yan uwanmu...
Malamar Da Ta Haura Shekaru 20 Ta na Haurawa Rafi Domin yin Da’awa

Malamar Da Ta Haura Shekaru 20 Ta na Haurawa Rafi Domin yin Da’awa

Labarai
An  bayyana labarin wata malama a Kano mai suna Khadija Muhammad, wacce ta shafe fiye da shekaru 21 tana haura rafi domin koyar da mata ilimin addini kyauta a kauyen Dan Shaye, karamar hukumar Rimin Gado. Wannan kyakkyawan aiki nata ya jawo hankalin jama'a, wanda hakan ya sa aka fara ba ta goyon baya da tallafi.Malama Khadija ta bayyana cewa ta fara wannan aikin ne bayan ta ga bukatar taimako daga mata a kauyen, inda ta ke tsallake rafi kowanne lokaci domin kawo ilimin addinin Musulunci ga matan aure. Ta ce, "Wata kawata ta nemi taimakona don koyar da mata dokokin addinin musulunci, wanda zai inganta rayuwarsu." A halin yanzu, gwamnatin Kano ta fara daukar mataki tare da bayar da umarnin gina makarantar Sakandare a kauyen Dan Shaye, wanda hakan zai taimaka wajen inganta ilimi a wannan...
Kwamitin Binciken Gobarar Tankar Fetur a Jigawa Ya Mika Rahotonsa ga Gwamnati

Kwamitin Binciken Gobarar Tankar Fetur a Jigawa Ya Mika Rahotonsa ga Gwamnati

Labarai
Daga Jigawa - gwamnatin Jigawa ta karbi rahoton kwamitin da ta kafa domin binciken faduwar tankar fetur da ta faru a jihar, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dama. Shugaban kwamitin, DIG Hafiz Muhammad Inuwa mai ritaya, ya bayyana cewa rahoton ya kunshi shawarwari masu muhimmanci da za su taimaka wajen kare rayuka a nan gaba.A cikin rahoton, an bayyana cewa mutane 209 ne suka rasu a hadarin da ya faru a kauyen Majiya, karamar hukumar Taura. Har yanzu, mutane 38 na kwance a asibiti, yayin da mutane 86 suka samu sauƙi kuma sun koma gida.DIG Inuwa ya sanar da cewa kwamitin ya bayar da shawarwari da suka haɗa da tabbatar da cewa tankokin fetur suna dauke da kayan kariya da za su hana mai zubewa idan an fadi tanka. Ya ce, binciken ya nuna cewa wasu motocin dakon mai ba su da kayan kariya,...