
Yaki zai Koma Baya: Ana Koƙarin Lallaɓa Tinubu Ya Saki Kasurgumin Dan Ta’adda
Yaki zai Koma Baya: Ana Koƙarin Lallaɓa Tinubu Ya Saki Kasurgumin Dan Ta'addaDaga FCT, Abuja- A cikin wani sabon labari, an fara ƙoƙarin tunkarar shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, da roƙon ya saki Nnamdi Kanu, wanda aka kama a shekarar 2021. Rochas Okorocha, tsohon gwamnan jihar Imo, ya bayyana wannan roƙon a yayin bikin bankwana da marigayi Sanata Ifeanyi Uba a Abuja.Okorocha ya yi kira ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da ya isar da wannan sako ga Tinubu, yana mai cewa hakan zai zama wata hanya ta karrama Sanata Uba, wanda ya sha rokon gwamnati ta saki Kanu kafin rasuwarsa."Idan aka saki Nnamdi Kanu, mu a kabilar Ibo za mu koma gida mu daidaita lamuramu," in ji Okorocha. A cewarsa, wannan mataki zai taimaka wajen inganta zaman lafiya a yankin.Duk da haka, hukuma...