Gyaran Matatu: Tinubu Ya Yabi Buhari, Za a Gyara Matatar Kaduna
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jin dadinsa kan fara gyaran matatar man Najeriya da ke Fatakwal, inda ya yabi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa kokarinsa na farfado da matatun man kasar. A yau Talata, 26 ga watan Nuwamba, 2024, kamfanin NNPCL ya sanar da cewa matatar Fatakwal ta fara aiki.
Tinubu ya bayyana cewa gwamnatin Buhari ta yi matuƙar ƙoƙari wajen dawo da matatun man Najeriya cikin aiki. A cikin wani sakon da hadiminsa, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafinsa na Facebook, Tinubu ya ce, "Zan ci gaba da ƙoƙarin kawar da kallon raini da ake yi wa Najeriya a matsayin ƙasa mai arzikin mai da ta gaza samar da matatu."
Shugaba Tinubu ya yi kira ga NNPCL da su mayar da hankali wajen gyara matatun man Kaduna da Delta, domin tabbatar da cewa dukkan matatun man Najeriya ...








