
An Shiga Fargaba Bayan Harin Sojoji Kan ‘Yan Ta’adda Ya Hallaka Bayin Allah
Ana fargaba cewa harin da sojoji suka kai domin fatattakar 'yan ta'adda a jihar Katsina ya salwantar da rayukan fararen hula. An ruwaito cewa mutane da dama sun kwanta dama, yayin da wasu da yawa suka samu munanan raunuka.Harin da sojojin sama suka kai a kauyen Shuwa da ke karamar hukumar Faskari ya jawo cece-kuce, inda wasu ke zargin cewa an kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba. Gwamnatin jihar Katsina ta musanta wannan zargi, inda ta ce sojojin sun kai harin ne bayan sun tabbatar da cewa 'yan ta'adda ne a wurin.Rahotanni sun nuna cewa harin ya janyo asarar rayuka da dama, ciki har da mata da kananan yara. Wani mazaunin kauyen Shuwa ya shaida cewa: "Sojojin sun jefa bam ne a kanmu, ba tare da sun san ko mu 'yan ta'adda ne ko ba mu ba. Mun rasa mutane da dama, ciki har da 'yan uwanmu...