Kwamitin APC Ya Fara Zaman Sulhu, An Dauko Hanyar Sasanta ‘Yan Jam’iyya
Jumma'a, Disamba 06, 2024 - Jam'iyyar APC ta fara kokarin haɗa kan mambobinta a jihar Adamawa domin gyara siyasarta a shekarar 2027. Wannan mataki ya biyo bayan kafa kwamitin sulhu na mutum takwas wanda ya haɗa da sanatan jihar da kuma manyan 'yan siyasa.
A cikin wata hira da manema labarai, Sanata Mohammed Mohammed Mana ya bayyana cewa kwamitin sun kammala shirin da zai tabbatar da cewa APC ta kwace Adamawa daga jam’iyyar adawa ta PDP. Ya ce, "Adamawa jiha ce mai muhimmanci, kuma mun kuduri aniyar ganin APC ta samu mafi yawan kujeru a 2027."
Kwamitin sulhun ya zauna a Yola, inda suka tattauna kan hanyoyin da za su bi domin magance kalubalen da jam'iyyar ke fuskanta a jihar. Hakanan, sun yi ganawar sirri domin gano yadda za su warware rikice-rikicen da suka taso a tsakanin mambobin j...








