Gobara Ta Yi Ajalin Ma’aurata a Jihar Kano
Wani mummunan ibtila'i ya faru a jihar Kano, inda wani magidanci da matarsa suka rasu sakamakon gobarar da ta tashi a unguwar Rangaza, karamar hukumar Ungogo. Wannan lamari ya jawo babban alhini a cikin al'umma.Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar ma'auratan, Muhammad Uba, mai shekaru 67, da matarsa Fatima Muhammad, mai shekaru 52. Jami'in hulɗa da jama'a na hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya bayyana cewa ma'auratan sun mutu ne sakamakon raunuka da hayaƙin da suka shaƙa.A cewar Saminu, hukumar ta samu kiran gaggawa daga wajen mazauna unguwar da misalin karfe 01:45 na tsakar dare. Jami'an hukumar sun yi sauri zuwa wurin, inda suka iso a lokacin da aka riga an shawo kan gobarar, amma sun tarar da ɗakuna biyu sun ƙone."Lokacin da muka isa, mun tarar da ma'auratan suna fu...








