Rashin Ilimi a Arewa: Manyan Kalubale da Suka Shafi Yara Miliyan 15
Arewacin Najeriya na fuskantar manyan kalubale a fannin ilimi, inda yara miliyan 15 ba sa samun damar zuwa makaranta. Wannan rahoto ya bayyana cewa, matsalolin da suka fi shafar yara a wannan yanki sun hada da rashin tsaro, talauci, da al’adun gargajiya.
Mastalar tsaroRashin tsaro na daga cikin manyan dalilan da ke hana yara zuwa makaranta, musamman a jihohin Borno, Yobe, da Adamawa. Hare-haren Boko Haram sun tilasta rufe makarantu da dama, wanda hakan ya jawo hijirar dalibai da kuma lalata ginin makarantu. Rahoton Human Rights Watch ya nuna cewa, wannan matsalar ta jawo gwamnoni da dama sun rufe makarantu domin kare lafiyar dalibai.Talauci A Arewa
Talauci yana daga cikin matsalolin da ke jawo rashin ilimi a Arewa, inda rahoton Bankin Duniya ya nuna cewa sama da kashi 70% na al’umma...








