Gwamna Abba Ya Nada Sabbin Kwamishinoni, Hadimin da Aka Tsige Zai Dawo
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya miƙa sunayen mutane shida ga majalisar dokokin jihar domin tantance su a matsayin sababbin kwamishinoni. Wannan mataki ya biyo bayan sauya wasu mukamai a gwamnatinsa, wanda ya fara aiwatarwa makon da ya gabata.Sunayen da gwamnan ya tura sun haɗa da tsohon shugaban ma'aikatar fadar gwamnatin jihar, Shehu Wada Sagagi, wanda aka sauke a makon da ya gabata, da sauran sabbin mutane kamar Dr. Dahiru Hashim, Ibrahim Wayya, Dr. Isma’il Dan Maraya, Gaddafi Shehu, da Abdulkadir AbdulSalam.Gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na nada kwamishinoni ya biyo bayan dawowarsa daga tafiya kasashen waje, inda ya ce tafiyar ta kasance mai amfani tare da buɗe sababbin damammaki ga jihar Kano. A cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Abba ya nuna fatan cewa m...








