Ana Tsaka da Jimamin Mutuwar yara, Wani ibtila’i ya sake faruwa a Ibadan
Al'ummar jihar Oyo sun shiga cikin juyayi bayan gobara mai ƙarfi da ta tashi a kasuwar sayar da kayan gyara ta Araromi, dake Agodi Gate a Ibadan. Wannan gobara ta yi sanadiyyar mutuwar yara 32 a wani taron nishaɗi da aka shirya a wannan yanki.Gobarar ta tashi da misalin karfe 2 na safiyar wannan rana, inda ta haifar da mummunar asara ga 'yan kasuwa da dama. Har zuwa yanzu, hukumar kashe gobara ta jihar Oyo na ci gaba da ƙoƙarin shawo kan wutar, yayin da aka nemi a kawo masu agaji don taimakawa wajen kashe gobarar.Babban manajan hukumar kashe gobara, Akinyemi Akinyinka, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa gobarar ta laƙume kadarorin 'yan kasuwa da suka kai miliyoyin Naira. Ya bukaci motocin ruwa su kawo agaji saboda gobarar tana ci gaba da yaɗuwa fiye da yadda aka zata.Har yanzu b...








