MURIC Ta Bukaci Wike Ya Mayar da Injiniya Hadi Kan Mukaminsa
Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bayyana damuwarta kan dakatar da Injiniya Shehu Ahmad Hadi daga mukaminsa na shugaban hukumar raya Abuja (FCDA), tana mai kira ga ministan Abuja, Nyesom Wike, da ya dawo da Hadi kan mukaminsa.
A wata sanarwa da Daraktan MURIC, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar, kungiyar ta ce rashin bayyana dalilin dakatar da Hadi ya nuna rashin bin ka'ida da rashin adalci daga Wike. Ta kuma jaddada cewa Hadi mutum ne mai kyakkyawar kwarewa wanda ya rike mukamin kwamishinan ayyuka a jihar Gombe ba tare da samun matsala ba.
MURIC ta yi nuni da cewa, "Idan ana so a tabbatar da gaskiya, ya kamata a fadawa Injiniya Shehu Hadi dalilin dakatar da shi." Hakanan, kungiyar ta zargi Wike da yin matakai da ba su dace ba, ciki har da rushe gidaje da nada mutanen yankinsa mu...








