Sheikh Albaniy Ya Yi Kira ga Adalci Kan Zargin Shugaban Nijar Tchiani
Malamin Musulunci, Sheikh Adam Muhammad Albaniy Gombe, ya soki zarge-zargen da Shugaban Nijar, Abdourahamane Tchiani, ya yi, inda ya ce zargin na Tchiani yana bukatar a duba shi da kyau kafin a yarda da shi. Sheikh Albaniy ya bayyana cewa Tchiani yana iya yin kuskure kamar yadda duk wani dan adam zai iya yi, domin ba mala'ika ba ne. Wannan jawabin ya biyo bayan zargin da Tchiani ya yi na cewa Najeriya na hadin gwiwa da Faransa domin kawo cikas ga kasarsa ta Nijar.A cikin wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Sheikh Albaniy ya bayyana cewa zarge-zargen da aka yi suna haifar da hayaniya da rigima, yana mai cewa akwai bukatar a yi bincike mai zurfi kafin a yanke hukunci.Malamin ya kuma jaddada cewa fadar shugaban kasa ta bakin Nuhu Ribadu ta karyata zargin da Tchiani ya yi,...








