Kungiyar Arewa Ta Nemi A Biya Diyya ga Iyalin Wadanda Sojoji Suka Hallaka a Sakkwato
Kungiyar Arewa ta bayyana damuwa game da hare-haren da sojojin sama suka kai wa fararen hula a jihar Sakkwato, inda aka kashe mutum 10 a kauyen Silame. Wannan lamari ya jawo fargaba a tsakanin dattawan yankin, wanda suka yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi bincike kan wannan al'amari.Bello Sani Galadanci, jami’in hulda da jama'a na kungiyar ACF a Kano, ya bayyana cewa ya zama wajibi a biya diyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu. Ya ce, "Wannan kisan ba za a lamunta ba, kuma ya kamata a dauki mataki mai kyau."Kungiyar ta yi kira ga gwamnatin Bola Tinubu da ta duba dalilin da ya sa aka kai hare-hare kan fararen hula. Galadanci ya bayyana cewa irin wannan lamari ya faru a Tudun Biri, inda al'ummar ba su ji ba, ba su gani ba, suna cikin zaman lafiya kafin a kai musu hari.ACF ta nuna cew...








