‘Yan Bindiga Sun Saka Haraji Mai Tsoka a Zamfara, Al’umma na Fuskantar Barazana
Rahotanni sun bayyana cewa ƴan bindiga sun sanya haraji mai tsoka kan mutanen ƙauyukan Tsafe ta Yamma a jihar Zamfara, lamarin da ya jefa al'umma cikin fargaba da tashin hankali. Tsagerun, wadanda ke karkashin jagorancin wani mutum da aka fi sani da Danisuhu, sun sanya harajin N172,700,000 ga ƙauyuka 25 a wannan yankin.
Wannan haraji ya tilastawa jama'a yin ƙaura daga gidajensu saboda fargabar tashin hankali da zai biyo baya. Harajin ya shafi ƙauyuka da dama, inda aka bukaci kowanne ƙauye ya biya kudi da kayayyakin noma, wanda hakan ya haifar da rashin jin daɗi a tsakanin mazauna yankin.
Masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayyana cewa sanya wannan haraji ya jefa al'ummar ƙauyukan cikin mawuyacin hali na rashin tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziki. Rahotanni sun nuna cewa...








