Daliba Ta Jagoranci Harin Kisan Malaminta a Kwalejin Kano
Wata daliba a Kwalejin Polytechnic ta Kano ta jagoranci yunkurin kai hari kan wani malami mai suna Aliyu Hamza Abdullahi. Wannan lamari ya faru ne a cikin ofishin malamin, inda dalibar tare da saurayinta suka yi yunkurin sare shi.A cewar hukumar makarantar, dalibar, wacce ba a saki sunanta ba, ta yi wannan hari ne bisa dalilin da ta ke ganin malamin ya hana ta canja kwas din karatu zuwa sashen da ta fi so. Duk da cewa an shaida mata cewa makinta bai kai matakin da ake bukata don canjin ba, wannan dalili ya zama sanadin tashin hankali.Jami’in hulɗa da jama’a na kwalejin, Auwal Isma’il Bagwai, ya tabbatar da faruwar wannan lamarin a wani taron manema labarai. Ya bayyana cewa yayin da malamin ke kula da ɗalibai a ofishinsa, dalibar ta shigo tare da saurayinta, inda saurayin ya fito da adda ya...








