Hukumar DSS Ta Mamaye Majalisar Dokokin Jihar Legas
A ranar Litinin, 17 ga watan Fabrairu 2025, jami’an Hukumar Tsaro ta DSS tare da 'yan sanda sun mamaye majalisar dokokin jihar Legas. Wannan lamari ya faru ne a safiyar wannan rana, inda aka rufe ofishin shugabar majalisar, Mojisola Meranda, da mataimakinta da sakataren majalisar a Alausa, Ikeja.Rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaron sun shiga zauren majalisar da misalin karfe 10:00 na safe, yayin da suke gudanar da bincike a cikin yankin. Hakan ya biyo bayan korafin tsohon shugaban majalisar, Mudashiru Obasa, wanda ya shigar da kara a kotu yana kalubalantar tsige shi daga mukamin.Shugabar majalisar, Rt. Hon. Meranda, ta isa majalisar tare da tawagarta da misalin karfe 11:15 na safe, yayin da aka rufe ofishin kakakin majalisar. Wannan yanayi na dauke hankali ya janyo cece-kuce a tsakani...








