Tashin Hankali a Abuja: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Matasa Biyu a Kuje
An samu tashin hankali a kauyen Gwargwada da ke yankin Kuje a Abuja, inda 'yan bindiga suka kashe matasa biyu da suka yi garkuwa da su. Lamarin ya faru ne sakamakon jinkirin biyan kudin fansa da aka bukata.Masu garkuwa sun nemi N1,000,000 a matsayin kudin fansa, amma iyalan wadanda aka sace sun tara N500,000 kacal. Wannan jinkirin biyan kudin ya jawo mummunan sakamako, inda aka kashe Mohammed Danladi da Nasiru Yusuf, tare da wani makiyayi da wata mata a kan hanyar Gwargwada-Rubochi.Sarkin Gwargwada, Ugbada Alhaji Hussaini Agabi Mam, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa har yanzu ba a gano gawarwakin matasan ba, amma suna kan gudanar da bincike. Alhaji Hussaini ya bayyana cewa wannan lamarin ya kasance mai matukar bakin ciki, musamman ganin yadda matasan suka rasa rayukansu saboda ...








