
Kin Biyan Haraji Babbar Matsala Ce A Abuja
Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana kin biyan haraji a matsayin babbar matsalar da yake fuskanta a Abuja. Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake duba wasu ayyukan raya kasa da gwamnatin tarayya ke gudanarwa a babban birnin, wadanda aka shirya kaddamarwa yayin bikin cika shekaru biyu da Shugaba Bola Tinubu ya yi kan karagar mulki.Daga cikin ayyukan da ministan ya duba har da Cibiyar Taro ta Kasa (AICC) da kuma fadada titin Obafemi Awolowo (N5) daga Life Camp zuwa Ring Road III. Sauran sun hada da gadoji da tituna da aka kammala a NICON Junction, gidajen alkalai, da kuma titin Wole Soyinka.Wike ya koka da yadda mazauna Abuja ke kin biyan haraji duk da irin kokarin da gwamnati ke yi na samar musu da ababen more rayuwa. Ya ce, "Mutane suna son ganin kyawawan abubuwa...