
Kotun Kaduna Ta Watsi da Ƙarar Tsige Sarkin Zazzau, Ahmed Nuhu Bamalli
Kotun daukaka kara da ke Kaduna ta yi hukunci kan karar da aka shigar domin neman tsige Sarkin Zazzau na 19, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli. Kotun ta bayyana cewa karar ba ta da inganci, kuma hakan ya sa a yanke hukuncin watsi da ita.Wazirin Zazzau, Ibrahim Mohammed Aminu, ne ya shigar da karar, yana mai zargin cewa ba a bi doka wajen nadin sarkin da tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi a shekarar 2020. Duk da haka, kotun ta ce an shigar da karar bayan lokacin da doka ta amince, wanda hakan ya sa ta watsi da ita.Wakilin Sarkin Zazzau ya bayyana cewa hukuncin kotun ya tabbatar da gaskiya, yayin da lauyan mai kara, Muhammed Tajudeen Muhammed, ya ce za su duba hukuncin kafin su yanke shawarar mataki na gaba.Hukuncin kotun ya nuna cewa masarautar Zazzau ta gamsu da wannan hukunci, wanda Khadi Muham...