Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje da Gonaki a Jihar Adamawa
A wani mummunan lamari, ambaliyar ruwa ta afka wa karamar hukumar Numan a jihar Adamawa, inda dubban mutane suka rasa muhallansu. Wannan lamari ya faru ne a daren 31 ga Agusta, lokacin da ruwa ya balle daga madatsar Kiri, wanda ya haifar da mummunar barna ga al’umma.Rahotanni sun nuna cewa ambaliyar ta yi sanadiyyar mutuwar mutum guda, yayinda gidaje da gonaki da dama suka rushe. Hukumomin bayar da agaji na gaggawa, NEMA da ADSEMA, sun gudanar da bincike a wuraren da ambaliyar ta afku, inda suka gano cewa an lalata gidaje a yankuna guda biyar, ciki har da Imburu, Zangun, da Lure.Bayan wannan lamari, hukumomin sun yi kira ga gwamnatin jihar da sauran masu ruwa da tsaki da su tura tallafi na gaggawa ga wadanda abin ya shafa. Wasu daga cikin wadanda suka tsinci kansu a cikin halin kaka-ni-ka-...








