Duniya

An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsakanin Isra’ila da Hezbollah

An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsakanin Isra’ila da Hezbollah

Duniya
Amurka ta sanar da cewa Isra'ila ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da mayakan Hezbollah da ke Kudancin Lebanon. Wannan yarjejeniyar ta biyo bayan shafe sama da shekara guda ana musayar wuta tsakanin dakarun Isra'ila da Hezbollah. Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bayyana cewa za a samu tsagaita wuta na tsawon watanni biyu, wanda zai ba da damar dakarun Isra'ila su janye daga Kudancin Lebanon, yayin da sojojin Lebanon za su mamaye wuraren da Hezbollah ke da iko. A martanin sa, shugaban Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce sojojinsa ba za su bata lokaci ba idan Hezbollah ta saɓa yarjejeniyar. Har yanzu, ba a ji daga kungiyar Hezbollah kan wannan yarjejeniyar ba, amma ba a sami wani alamar karya yarjejeniyar ba. Wakilin Amurka, Amos Hochstein, wanda ya jagoranci tattaunawar, ya bayyana...
Bayan Umarnin Kama Netanyahu, Isra’ila na Shirin Tsagaita Wuta a Lebanon.

Bayan Umarnin Kama Netanyahu, Isra’ila na Shirin Tsagaita Wuta a Lebanon.

Duniya
A halin yanzu, ana shirin tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da kungiyar Hisbullah a kasar Lebanon, bayan tsawon lokaci na kai hare-hare da juna. Wannan mataki na tsagaita wuta yana zuwa ne bayan umarnin kotun hukunta masu manyan laifuffuka ta ICC da ta bayar a makon da ya gabata, wato a kama tsohon firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu. Wakilin kasar Amurka, Amos Hochstein, yana jagorantar tattaunawar da ke gudana don kawo karshen rikicin da ke tsakanin Isra'ila da Hisbullah. Rahotanni sun nuna cewa Isra'ila ta nuna alamar amincewa da shirin tsagaita wutar, wanda zai kasance na tsawon kwanaki 60, domin lalubo hanyoyin da za su kawo karshen rikicin gaba daya. Hochstein ya bayyana cewa idan Isra'ila ta yi jinkirin amincewa da shirin, zai zare hannunsa daga tattaunawar. A yanzu haka, ...
Sojojin Nijar Sun Dora a Kan Aikin Najeriya: An Hallaka Yan Lakurawa

Sojojin Nijar Sun Dora a Kan Aikin Najeriya: An Hallaka Yan Lakurawa

Duniya
Daga Jamoriyar Nijar– Rundunar sojin Nijar ta tabbatar da cewa dakarunta sun hallaka 'yan ta'addan Lakurawa da suka tsallaka daga Najeriya. Wannan samame ya faru ne a yankin Illela na jihar Tahoua a ranar 21 ga Nuwamba, bayan da sojojin Najeriya suka fatattaki 'yan fashin daga cikin kasar, suna mai tabbatar da cewa sun tsallaka zuwa Nijar don tserewa daga harin. Rahotanni sun bayyana cewa sojojin Nijar sun gudanar da wannan aiki ne tare da hadin gwiwar jami'an tsaro, domin toshe yunkurin 'yan ta'addan da suka yi yunkurin tsallaka daga Najeriya. An ce Lakurawan sun kutsa cikin jamhuriyyar Nijar domin ci gaba da aikace-aikacen su na ta'addanci, wanda hakan ya jawo hankalin sojojin. A cikin rahoton da rundunar sojin Nijar ta fitar, an bayyana cewa 'yan ta'addan sun yi sanadiyyar kashe w...
Trump Ya Yiwa Najeriya Barazana kan Ci Gaba da Tsare Kasurgumin Dan Ta’addan IPOB?

Trump Ya Yiwa Najeriya Barazana kan Ci Gaba da Tsare Kasurgumin Dan Ta’addan IPOB?

Duniya
Trump Ya Yiwa Najeriya Barazana kan Ci Gaba da Tsare Kasurgumin Dan Ta'addan IPOB?Wani bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta na nuna zababben shugaban kasar Amurka, Donald Trump, yana neman gwamnatin Najeriya ta saki Nnamdi Kanu, shugaban kungiyar IPOB.A cikin bidiyon, an ji Trump na ba gwamnatin Najeriya wa'adin ta kwana na 31 ga Nuwamba ta saki Kanu ko ta fuskanci fushinsa. Ya kuma yi barazanar janye tallafin kiwon lafiya, kudi da na jin kai daga Najeriya, da kuma sanya takunkumi a kan kasar idan ba ta bi bukatarsa ba.Bincike ya nuna cewa bidiyon bogi ne, an tsakuro shi ne daga jawabin nasarar Trump da ya yi bayan ya lashe zaben Amurka a ranar 6 ga Nuwambar 2024. Wa'adin da ake zargin Trump ya sanya na ranar 31 ga Nuwamba ya sanya ayar tambaya kan sahihancin bidiyon domin Nuwamba na ...
Kotun ICC Ta Ba Da Sammacin Cafke Netanyahu Da Wasu Kwamandojin Hamas

Kotun ICC Ta Ba Da Sammacin Cafke Netanyahu Da Wasu Kwamandojin Hamas

Duniya
A wani mataki mai cike da cece-kuce, kotun manyan laifuffuka ta duniya (ICC) ta ba da sammacin cafke Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar, da kuma wasu kwamandojin kungiyar Hamas. Wannan mataki ya biyo bayan cigaba da zubar da jini da ake yi a Gabas ta Tsakiya tsakanin Isra'ila da Hamas tsawon lokaci. Kotun ta ce ta gaji da rikicin da ke kawo asarar rayuka da dukiyoyi, kuma ta yanke shawarar daukar mataki domin dakile shi. Wannan mataki da kotun ICC ta dauka ya jawo cece-kuce da suka daban-daban, inda wasu ke ganin yana da kyau domin kawo karshen rikicin, yayin da wasu ke ganin ba zai haifar da wani sakamako mai kyau ba.Kotun ta ce tayi Watsi da yunkurin isra'ila na kalubalantar iKon da Kotun ke da shi kan sauraron shari'ar Akwai bukatar a sam...
Shugaban ‘Yan Ta’addan Biyafara, Simon Ekpa, Ya Shiga Hannu An Tura Shi Kurkuku

Shugaban ‘Yan Ta’addan Biyafara, Simon Ekpa, Ya Shiga Hannu An Tura Shi Kurkuku

Duniya
Hukumomi a kasar Finland sun kama shugaban 'yan ta'addan Biyafara, Simon Ekpa, wanda ake zargi da jagorantar ta'addanci a kudu maso yammacin Najeriya.An kama Ekpa ne a ranar Litinin, 20 ga watan Nuwamba, 2024, bayan wata kotu a yankin Paijat Hame ta kasar Finland ta bayar da umarnin kama shi. Rahotanni sun nuna cewa an kama Ekpa ne tare da wasu mutane hudu da ake zargi da hannu a ta'addancin da ya addabi kudu maso yammacin Najeriya. Hukumar 'yan sandan Finland ta tabbatar da cewa an kama Ekpa ne bisa laifin jagorantar ta'addanci da tura matasa su kai hare-hare a Najeriya.Simon Ekpa ya zama shugaban 'yan ta'addan Biyafara tun bayan kama Nnamdi Kanu a kasar Kenya.An zargi Ekpa da hura wutar rikici da kai hare-hare kan jami'an tsaron Najeriya a kudu maso yammacin kasar.Hukumomin tsaro sun ...