Kakakin Majalisar Wakilai Ya Nemi Hadin Kan Jagorori don Tabbatar da Kudirin Haraji
Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, ya gudanar da ganawa da shugabannin shiyyoyin kasar nan guda shida da sakatarorinsu a majalisa, domin neman amincewa da kudirin harajin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gabatar. Wannan taron ya kasance ne a ranar Litinin, inda aka tattauna kan kudirorin gyaran dokar haraji guda hudu da ke jawo ce-ce-ku-ce daga sassan Najeriya.Abbas ya bayyana cewa yana da matukar muhimmanci a samu hadin kai daga 'yan majalisa domin tabbatar da cewa kudirin harajin ya samu nasara. A cewarsa, kudirin na da niyyar warware matsalolin tattalin arziki da kuma saukaka haraji ga talakawa da kananan 'yan kasuwa a kasar.A cikin taron, an samu wakilai daga arewacin Najeriya, ciki har da Sada Soli daga Arewa maso Yamma, Mukhtar Betara daga Arewa maso Gabas, da...








