Gwamnatin Tinubu Ta Kalubalanci Gwamnan APC Kan Dakatar da Shugabannin Kananan Hukumomi
Gwamnatin tarayya ta yi fatali da matakin Majalisar dokokin jihar Edo na dakatar da shugabannin kananan hukumomi guda 18 da mataimakansu. Ministan shari'a, Lateef Fagbemi, ya bayyana wannan martani, yana mai Allah wadai da matakin da Majalisar ta dauka.
Majalisar jihar Edo ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi ne bayan samun korafi daga gwamnan jihar, Monday Okpebholo, wanda ya zargi shugabannin da nuna rashin biyayya ga umarninsa na mika bayanan kudadensu. Fagbemi ya ce a hakikanin gaskiya, dokar Najeriya ba ta bai wa Majalisar ikon yin wannan dakatarwar.
Fagbemi ya jaddada cewa, “A karkashin wannan mulki na yanzu, gwamna ba shi da damar tsige kowanne shugaban ƙaramar hukuma.” Wannan hukunci ya takaita ikon gwamnonin jihohi daga tsoma baki cikin harkokin shugabannin ƙananan huk...








