Tinubu Ya Yi Murnar Shekara Biyu da Raba Mukamai 61 a Jami’o’i da Kwalejoji
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da nadin sababbin mambobi a majalisun gudanarwa na jami’o’i, kwalejojin ilimi, da kwalejojin fasaha a Najeriya. Wannan nadin ya shafi jami’o’i da cibiyoyin ilimi daga jihohi daban-daban na Arewa da Kudu, kuma ya ƙunshi mutane 61.Wannan mataki na nadin mukamai ya zo ne a cikin tsarin murnar cika shekara biyu a kan mulkin Tinubu. Ma’aikatar yada labarai ta fitar da sanarwar nadin a shafinta na X, inda ta bayyana cewa wannan yunkuri na nufin inganta shugabanci da gudanarwa a cibiyoyin ilimi domin dorewar ci gaban su.A cikin jerin sunayen wadanda aka nada, akwai jami’o’i kamar Jami’ar Kimiya da Fasahar Jiragen Sama ta Afirka da Jami’ar Jos, tare da wasu kwalejoji da cibiyoyin ilimi na tarayya.Shugaba Tinubu ya bayyana cewa wannan nadin na daga cikin mataka...








