Abun da mutane sukayi wa Bola Tinubu Bayan Sallar Juma’a a Legas
A ranar 3 ga watan Janairu 2025, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gudanar da Sallar Juma'a a babban masallacin jihar Legas, inda ya amsa gaisuwar ɗaruruwan Musulmi bayan kammala ibada. Wannan taron ya jawo hankalin jama'a, wadanda suka yi dafifi a cikin masallacin da kuma wajen sa.Bola Tinubu, wanda ke hutu a jihar Legas, ya ɗaga hannunsa ga mutane, yana nuna alamar amsa gaisuwar su kafin ya shiga mota ya koma gida. Bidiyon wannan taron ya bayyana yadda mutane suka yi farin ciki da kasancewar shugaban a wajen su.Mai taimaka wa shugaban kan harkokin soshiyal midiya, Dada Olusegun, ya wallafa bidiyon soyayyar da aka nuna wa Tinubu a shafinsa na X, inda ya bayyana cewa shugaban kasa ya amsa gaisuwar masu ibada.Martanin mutane kan wannan taron ya bambanta, inda wasu suka bayyana goyon bayans...








