Jami’in Tsaro Ya Rasa Ransa Bayan Ceto Mutane 66 daga Hannun Ƴan Bindiga a Sokoto
A jihar Sokoto, an shiga cikin jimami bayan rasuwar wani jami'in rundunar tsaro wanda ya harbi kansa bisa kuskure. Wannan lamari ya faru ne a ranar Laraba, 8 ga watan Janairu, bayan wani aikin haɗin gwiwa da ya kai ga ceto mutane 66 da ƴan bindiga suka sace.Mai ba Gwamna Ahmed Aliyu shawara kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya tabbatar da wannan lamari, inda ya bayyana cewa jami'in ya rasa ransa ne bayan da bindigarsa ta tashi a lokacin da yake dawo daga aikin ceto. Jami'in tsaron, wanda ba a bayyana sunansa ba, ya harbi kansa a Sokoto, jim kaɗan bayan an kammala aikin ceto. Kanal Usman ya ce, “Lamarin ya faru ne jim kaɗan bayan sun dawo sansaninsu daga aikin ceto. Yana tare da bindigarsa, sai ta tashi bisa kuskure ta harbe shi, sai ya rasu nan take."An gudanar da wannan ...








