Author: Aisha

Matsalar Kuɗi: Shugaban NNPCL Ya Kauracewa Majalisa

Matsalar Kuɗi: Shugaban NNPCL Ya Kauracewa Majalisa

Labarai
Shugaban kamfanin man fetur na ƙasa (NNPCL), Bayo Ojulari, ya fuskanci matsala mai tsanani daga kwamitin binciken asusun majalisar dattawa, bayan da aka bayyana rashin daidaito a cikin bayanan kuɗin kamfanin.Majalisar ta bayyana cewa akwai bambanci na kuɗi na Naira tiriliyan 210 wanda NNPCL ya bayar a rahoton kuɗinsa, amma ba a gabatar da takardun shaida da suka tabbatar da wannan kuɗin ba. Sanatoci sun yi barazanar cewa idan shugaban kamfanin ya gaza bayyana a gaban su, za su iya ɗaukar matakan hukunci da suka haɗa da kama shi da gurfanar da shi a kotu.Shugaban kwamitin majalisar, Sanata Aliyu Wadada, ya jaddada cewa wannan gayyata ba zaɓi ba ne, yana mai cewa majalisar tana da ƙarfin doka don kiran duk wani jami’in gwamnati da ke guje wa bayar da bayanai da aka buƙata. Ya bayyana cewa ko...
Addu’ar Neman Tsari Daga Sharrin Mutane

Addu’ar Neman Tsari Daga Sharrin Mutane

Addu’a
Assalamualaikum warahmatullahi wabarakatuhu, barkan mu da war haka, sannu ku da kasancewa tare da mu a Cikin wannan shafin namu a dai dai wannan lokacin A cikin duniya mai cike da kalubale da sharruka daban daban, addu'a tana da matukar muhimmanci ga kowanne Musulmi. Addu'a tana bayar da kariya, da kuma taimaka mana wajen samun tsari daga sharrin mutane. Rubutun mu zai yi nazari kan, addu'oin da ya kamata mu dinga Yi, da kuma mahimmancin sa da kuma hanyoyin da za mu iya amfani da ita wajen neman tsari daga sharrin mutane.Mahimmancin Addu'aAddu'a, tana matsayin ibada, tana da matukar daraja a cikin addinin Musulunci. Ta hanyar addu'a, muna bayyana bukatunmu ga Ubangiji Allahu SWT, muna neman taimako daga gare shi, da kuma neman kariya daga sharrin da zai iya zuwa daga mutane. Addu'a ...
Oyedepo Ga Mambobin Cocinsa: “Kada Ku Sake Zaben Wauta a 2027”

Oyedepo Ga Mambobin Cocinsa: “Kada Ku Sake Zaben Wauta a 2027”

Labarai
Babban malamin addinin Kirista, Bishop David Oyedepo, ya yi kira ga mambobin cocin Living Faith Church, da aka fi sani da Winners Chapel, da su yi amfani da hankali da basira wajen zaben 2027.A yayin wani wa'azi da ya gabatar, Oyedepo ya tambayi wadanda suka sayar da kuri'unsu a zaben da ya gabata ko kudin da aka ba su har yanzu yana nan. Ya kuma yi Allah wadai da lalacewar tsarin raba mukamai a kasar."Kudin da aka ba ku a zaben da ya gabata, ina da tabbacin har yanzu yana nan. Ban tsammanin wani memba na wannan coci zai sake yin wauta a wannan karon ba. Yau ana yayata tikitin Musulmi da Musulmi, gobe kuma za a yayata Fulani da Fulani, jibi kuma gwamnoni za su mika wa 'yan uwansu, saboda an riga an lalata tsarin raba mukamai...." in ji Oyedepo.Kalaman Oyedepo sun jawo ce-ce-ku-ce a shafuka...
APC Na Neman Jan Gwamnoni Biyar Zuwa Jam’iyyarta

APC Na Neman Jan Gwamnoni Biyar Zuwa Jam’iyyarta

Labarai
Jam'iyyar APC mai mulki ta bayyana cewa tana ƙoƙarin jawo gwamnoni biyar zuwa cikin jam'iyyarta, a daidai lokacin da wasu manyan 'yan siyasa da 'yan majalisa ke sauya sheƙa zuwa APC, tare da mara wa shugaba Bola Tinubu baya domin sake tsayawa takara a 2025.Wannan bayani ya fito ne a wata tattaunawa ta musamman da jaridar Punch ta yi da mataimakin shugaban jam'iyyar APC na ƙasa a shiyyar Kudu maso Gabas, Dr. Ijeoma Arodiogbu.A cewar Arodiogbu, gwamnonin da ake sa ran zasu sauya sheƙa sun hada da na jihohin Bayelsa, Ribas, Filato, Kano, da kuma Abia ko Enugu. Ya ce, "A cikin watanni biyu masu zuwa, za ku ga sun shigo jam'iyyar a hukumance."Wannan ci gaba na zuwa ne bayan da gwamnan jihar Akwa Ibom, Umo Eno, ya sauya sheƙa zuwa APC tare da 'yan majalisa da kuma dukkan shugabannin jam'iyyar PD...
APC Ta Yi magana ka Shigar Kwankwaso Jam’iyyar

APC Ta Yi magana ka Shigar Kwankwaso Jam’iyyar

Siyasa
Jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ta karyata rade-radin da ake yadawa cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, jagoran jam'iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), na shirin komawa jam'iyyar mai mulki.Jita-jitar ta yi ƙarfi musamman bayan murabus din Abdullahi Ganduje daga muƙamin shugaban jam'iyyar APC na ƙasa.  Sai dai a wata tattaunawa da Channels Television a ranar Lahadi, Sakataren Yaɗa Labaran APC na Ƙasa, Felix Morka, ya musanta wannan batu, yana mai cewa babu wata tattaunawa da ake yi tsakanin jam'iyyar da Kwankwaso kan batun shigarsa APC."Jam'iyyar da nake magana a madata ba ta ce komai ba game da yiwuwar Kwankwaso ya shigo," in ji shi lokacin da aka tambaye shi game da yiwuwar tsohon gwamnan Kano ya sauya sheƙa.Ya ƙara da cewa, "Ba mu yanke wani hukunci ba kuma ba za mu iya yanke...
Jonathan Yayi magana Kan Shirin Takaran Shugaban Ƙasa a 2027

Jonathan Yayi magana Kan Shirin Takaran Shugaban Ƙasa a 2027

Labarai
Tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan ya karyata wani saƙo da ya yaɗu a shafukan sada zumunta, musamman ma a Instagram, wanda ke nuna cewa yana shirin sake tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.  Kakakin tsohon shugaban ƙasar, Ikechukwu Eze, ya bayyana cewa saƙon ƙarya ne kuma Jonathan ba shi da hannu a ciki.Saƙon, wanda aka wallafa a wani shafi na Instagram mai ɗauke da sunan Goodluck Jonathan, ya soki shugabannin Najeriya na yanzu, yana mai zarginsu da "yin kamar suna barci."  Ya kuma yi kira ga 'yan ƙasa da su zaɓi shugabanci na gari a 2027.Saƙon ya ƙunshi kiɗa da wani hoto da ake zargin an ƙirƙira ta hanyar amfani da fasahar AI, wanda ke nuna Jonathan yana gaisawa da tsohon Shugaban Amurka Donald Trump.Eze ya bayyana cewa Jonathan ba shi da shafi a Instagram, kuma saƙon ba daga g...
Hare-Hare a Benue: An Kashe Mutane 26 a Makurdi da Katsina-Ala

Hare-Hare a Benue: An Kashe Mutane 26 a Makurdi da Katsina-Ala

Labarai
An kashe akalla mutane 26 a hare-haren da 'yan bindiga suka kai a kananan hukumomin Makurdi da Katsina-Ala na jihar Benue a daren ranar Alhamis.  Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun shiga gidaje tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na safe, ɗauke da makamai, inda suka yi wa mutane kisan gilla.A yankin Mtswenem da Akondotyough Bawa da ke yankin North Bank a Makurdi, an kashe mutane 25.  Wani mutum kuma ya rasa ransa a wani harin daban da aka kai a Kenvanger da Agbami a gundumar Mbatyula ta ƙaramar hukumar Katsina-Ala.Shaidu sun bayyana cewa maharan sun shiga gidaje suna harbi ba kakkautawa, inda suka kashe mata da yara.  Wasu mazauna yankin sun tsere, amma da yawa sun rasa rayukansu.  An ruwaito cewa wasu daga cikin waɗanda suka jikkata sun mutu a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.A Katsina-Ala, ...
Wike Ya Kare Sanya Sunan Tinubu a Cibiyar ICC, Ya Maida Martani Ga Masu Sukan

Wike Ya Kare Sanya Sunan Tinubu a Cibiyar ICC, Ya Maida Martani Ga Masu Sukan

Labarai
Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya kare matakin da ya ɗauka na sanya wa Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa (ICC) da ke Abuja sunan Shugaba Bola Tinubu.  Wike ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Juma'a yayin ƙaddamar da kammala aikin hanyar gefen hagu mai tsawon kilomita 15 daga Ring Road I zuwa kwanar Wassa.Martanin na Wike ya biyo bayan ce-ce-ku-cen da ya ɓarke a shafukan sada zumunta bayan an sanya wa cibiyar sunan shugaban ƙasa.  Wasu 'yan Najeriya sun soki matakin, yayin da wasu kuma suka yi Allah-wadai da kashe Naira biliyan 39 da aka yi wajen gyaran ginin.Wike ya bayyana mamakin yadda wasu ke sukar sanya sunan Tinubu a cibiyar, yana mai cewa filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe ba Azikiwe ne ya gina shi ba, haka ma filin wasanni na Moshood Abiola ba Abiola ne ya gina shi ba.  Ya...
Azumi da Addu’a Domin Nema Mafita Kan Karancin Abinci a Najeriya

Azumi da Addu’a Domin Nema Mafita Kan Karancin Abinci a Najeriya

Labarai
Ma'aikatar Noma da Samar da Abinci ta Tarayya ta ayyana kwanaki uku na azumi da addu'a domin neman taimakon Allah kan ƙalubalen karancin abinci da ake fama da shi a ƙasar.  Wannan sanarwar ta fito ne daga ofishin Daraktan Kula da Ma'aikata, Adedayo Modupe, a ranar 11 ga watan Yuni.An ƙarfafa ma'aikatan ma'aikatar baki ɗaya da su shiga wannan azumi da addu'a, wanda za a gudanar a babban ɗakin taro na hedikwatar ma'aikatar da ke Area 11, Garki, Abuja, daga ƙarfe 12:00 na rana zuwa 12:30 na rana.Za a fara azumin ne a ranar Litinin, 16 ga watan Yuni, sannan a ci gaba a ranakun 23 da 30 ga watan Yuni.  Taken zaman addu'ar shi ne "Shiga cikin addu'a domin kare ƙasa da neman cigaba."A cewar sanarwar, an shirya wannan addu'a ne domin neman shiriyar Allah da taimakonsa a ƙoƙarin da gwamnatin tarayy...
An Raba Masoya Biyu a Kaduna Bayan Kotun Shari’a Ta Haramtawa Saurayi Zuwa Unguwar Budurwa

An Raba Masoya Biyu a Kaduna Bayan Kotun Shari’a Ta Haramtawa Saurayi Zuwa Unguwar Budurwa

Labarai
Wata kotun Shari'a da ke Rigasa a jihar Kaduna ta raba wasu masoya biyu, Salisu Salele da Bilkisu Lawal, bayan da kotun ta haramtawa Salisu zuwa unguwarsu Bilkisu, ko kuma yin wata hulɗa da ita.  Hukuncin ya biyo bayan korafin da iyayen Bilkisu suka shigar a gaban kotun, suna neman a raba ɗansu da Salisu.Alƙalin kotun, Malam Salisu Abubakar-Tureta, ya yanke hukuncin bayan masoyan sun amince su rabu a gaban iyayensu da kuma shugaban unguwar.  Daga ranar da aka yanke hukuncin, Salisu ba zai sake zuwa layinsu Bilkisu ba, ko kuma ya kirata a waya. Yin hakan zai jawo masa fushin hukuma."Daga yau, Salisu ba zai kira ko gana da Bilkisu ba, an hana shi bin unguwarsu ko tsayawa kusa da gidan su Bilkisu," in ji alkalin. "In an kama shi yana kiranta ko ganinta a ko’ina, za a ɗauki matakin da ya dace ...