Hisbah Ta Kwato Kudi Sama da Naira Biliyan 200 a Kano
Rundunar ƴan sandan Musulunci watau Hisbah a jihar Kano ta bayyana cewa ta gudanar da ayyuka masu yawa a shekarar 2024, inda ta ƙwato kudi har Naira biliyan 212.3 ga masu su na halal. Mataimakin babban kwamandan Hisbah, Mujahideen Aminudden, ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a Kano.
Mujahideen ya ce, a shekarar da ta gabata, rundunar ta karbi korafe-korafe guda 16,939, waɗanda suka shafi rikice-rikicen aure, kasuwanci, gado, da kuma basussuka. Daga cikin waɗannan, an samu nasarar warware rikice-rikice guda 7,884, wanda hakan ya taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al'umma.
Hukumar ta ce, bayan karɓar kudaden, ta bai wa masu su na halal ba tare da ɗaukar ko sisi ba, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinta na tabbatar da adalci da inganta rayuwar al'umma. Muja...








