An Harbe Limamin Da Ya Ke Tallafawa Yan Luwadi a Afirka ta Kudu
An harbe Imam Muhsin Hendricks, wanda aka san shi a matsayin limami na farko da ya bayyana kansa a matsayin dan luwadi, a kusa da birnin Gqeberha a Afirka ta Kudu. Wannan lamari ya faru ne a ranar Asabar, 15 ga watan Fabrairu, 2025, lokacin da wasu mutane biyu masu rufe fuska suka kai masa hari.Rahotanni sun nuna cewa Imam Hendricks yana cikin mota tare da wani mutum lokacin da aka tare su, daga bisani aka bude wuta a kansu. Bayan harbin, wadanda suka kai harin sun tsere, kuma an tabbatar da cewa Imam Hendricks ya rasu a wannan hari.‘Yan sanda sun fara bincike kan wannan kisan, suna neman gane dalilin da ya sa aka yi wannan mummunan hari. Jami’an sun bayyana cewa suna rokon duk wanda ke da bayani akan lamarin ya tura su da shi.Wata kungiya mai suna ILGA ta yi Allah wadai da wannan kisan, t...








