Gwamna Adeleke Ya Janye Gargadin Tinubu, Zai Gudanar da Zabe a Osun
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya bayyana cewa zaben kananan hukumomi da aka shirya gudanarwa a ranar 22 ga watan Janairu 2025, zai ci gaba da gudana duk da gargadin da Atoni-janar na Tarayya, Lateef Fagbemi, ya yi. Gwamna Adeleke ya ce dimokuradiyya tana bin doka, kuma ba wanda zai iya takawa dokar kotu.A yayin da yake amsa gargadin, gwamnan ya jaddada cewa zaben zai kasance bisa doka, tare da kira ga jama'a da su zauna lafiya a lokacin zaben. Fagbemi ya gargadi cewa gudanar da zaben ba zai yi inganci ba saboda hukuncin kotu da ya soke zaben kananan hukumomin da tsohon gwamna Adegboyega Oyetola ya gudanar.Gwamna Adeleke ya bayyana cewa duk da wannan gargadi, zai gudanar da zaben domin tabbatar da dimokuradiyya a jihar. Ya kuma yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su kiyaye doka d...








