Sabuwar Zanga-Zanga Ta Barke a Kano: Jami’an Tsaro Sun Tashi Tsaye
Sabuwar zanga-zanga ta ɓarke a cikin birnin Kano, inda masu zanga-zangar suka taru a ƙarƙashin gadar Ƙofar Nasarawa. Wannan zanga-zangar ta faru ne ba tare da wani bayani na musamman game da musabbabin ta ba, wanda ya jawo hankali daga hukumomi da masu lura da al'amuran yau da kullum.Jami'an tsaro, ciki har da ƴan sanda da hukumar DSS, sun yi gaggawar zuwa wurin domin tarwatsa masu zanga-zangar. An yi amfani da barkonon tsohuwa wajen dakile zanga-zangar, yayin da jami'an tsaro suka sanya shamaki a hanyoyin da ke kaiwa Gidan Gwamnatin Kano.Jami'in hulɗa da jama'a na ƴan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an kama mutum 17 da ake zargin suna da hannu a zanga-zangar. Ya ce, "Rundunar ƴan sandan jihar Kano na son sanar da jama’a c...








