Matsalar Jam’iyyar LP: Ozigbo Ya Bayyana Makomar Peter Obi a Zaben 2027
A ranar Jumma'a, 28 ga Fabrairu, 2025, tsohon dan takarar gwamna a jihar Anambra, Valentine Ozigbo, ya bayyana damuwarsa kan halin da jam'iyyar Labour Party (LP) ke ciki, inda ya nuna cewa akwai alamu masu nuni da cewa jam'iyyar na fuskantar rugujewa. Ozigbo, wanda ya taya Peter Obi fafutukar neman shugaban Najeriya a zaben 2023, ya fice daga jam'iyyar saboda wasu dalilai da suka shafi nasarorin siyasa. Ya bayyana cewa tattaunawa tsakanin Peter Obi da wasu jam'iyyu sun yi nisa, a kokarin hadaka gabanin zaben 2027.A cewar Ozigbo, "Ba na ganin wata makoma ga LP a nan gaba." Ya kara da cewa ko da Peter Obi yana son sake neman kujerar, ba zai yi hakan a ƙarƙashin jam'iyyar LP ba.Hakanan, ya yi nuni da cewa akwai maganganu na yiwuwar hadaka da wasu jam'iyyun adawa, wanda hakan ya sa ya yanke sh...








