Kwankwaso Ya Halarta Taron Tattalin Arziki a Aso Villa
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamna da jagoran jam'iyyar NNPP, ya isa fadar shugaban kasa, Aso Villa, domin halartar babban taron tattalin arziki a Najeriya. Taron, wanda aka shirya tare da hadin gwiwar NatureNews da WEN Synergies, yana nufin tattauna hanyoyin inganta dajin Najeriya mai darajar Dala biliyan 2.Masana, masu zuba jari, da jami’an gwamnati sun taru a dakin taro na Banquet Hall domin nazarin hanyoyin da za a bi wajen inganta albarkatun daji da kuma rage tasirin canjin yanayi. Ana sa ran shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima za su halarci taron domin nuna goyon bayansu.Kwankwaso ya bayyana cewa taron yana da matukar muhimmanci wajen samar da tsarin da zai inganta tattalin arzikin Najeriya, tare da samar da ayyukan yi da kuma kula da muhalli. Haka...








