Shekarau Ya Bayyana Dangantakarsa da Kwankwaso, Ya Koka Kan Rashin Amincewa
Tsohon gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya bayyana kyakkyawar alaka da Sanata Rabiu Kwankwaso da Abdullahi Ganduje, duk da sabanin ra'ayi a fannin siyasa. A cikin wata hira da ya yi, Shekarau ya nuna damuwarsa kan yadda Kwankwaso ya ci amanarsa a lokacin da suka kafa kwamiti domin tsara tsarin zabe a shekarar 2019.Shekarau ya ce, "Kafin zaben 2019, mun kafa kwamiti da Kwankwaso, amma a karshe mun ji sunayen 'yan takara a kafafen sada zumunta ba tare da an tuntube mu ba." Ya bayyana cewa, wannan lamari ya jawo rashin jin dadin sa, yayin da ya tabbatar cewa yana da kyakkyawar alaka da Kwankwaso da Ganduje.A cikin maganarsa, Shekarau ya tuna lokacin da yake neman zabe a shekarar 2003, inda ya ce babu wanda ya yi tsammanin nasararsa. Ya ce, "A zaben 2007, har Muhammadu Buhari ya ki ...








