Majalisar Wakilai Ta Amince da Cire Haraji Daga Albashin Sojoji
Majalisar Wakilai ta Najeriya ta amince da wani muhimmin kudiri da ya shafi dakarun soja, wanda ke nufin cire harajin kudin shiga daga albashin su. Wannan kudiri an gabatar da shi ta hannun Kwamitin Kudi na majalisar, wanda shugaban sa, Abiodun Faleke, ya bayyana a lokacin da ake nazarin dokokin haraji da Shugaba Bola Tinubu ya mika ga majalisar.Faleke ya jaddada cewa cire harajin na da matukar muhimmanci domin girmama aikin da sojoji ke yi wajen kare lafiyar kasa. Ya bayyana cewa wannan mataki na kwamitin ya samu goyon bayan dukkan 'yan majalisar ba tare da wata gardama ba, saboda irin kokarin da sojojin ke yi wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a Najeriya.A yayin taron, Faleke ya ce:"Mai girma, kajakin majalisa da yan uwana a wannan wuri, kwamitinmu ya gabatar da kudiri kan cire hara...








