NiMet Ta Yi Hasashen Ruwan Sama a Kano da Sauran Jihohi
Hukumar Kula da Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar da cewa za a samu ruwan sama mai ƙarfi a sassan Arewa da Kudancin Najeriya a ranar Juma'a, 25 ga Yuli, 2025. Hasashen ya shafi jihohin kamar Kano, Katsina, Bauchi, da Borno, inda aka sa ran za a fuskanci tsawa da ruwan sama.A cikin sanarwar da NiMet ta fitar, an bayyana cewa daga safiyar ranar Juma'a, akwai yiwuwar haduwar hadari da yayyafi a Arewacin Najeriya, musamman a jihohin Jigawa, Gombe, Kaduna, da Adamawa. Daga yammaci zuwa dare, ruwan sama mai karfi zai sauka a jihohin Taraba, Sokoto, da Yobe.NiMet ta shawarci jama'a da su yi taka tsantsan, musamman a yayin tuki, domin kaucewa haɗurra da kuma guje wa fadowar reshen bishiyoyi yayin guguwa. Hakanan, hukumar ta bukaci kamfanonin jiragen sama da su duba rahoton yanayin filin...








