Author: Aisha

Sirrin Cin Jarabawa: Hanyoyi da Shawarwari

Sirrin Cin Jarabawa: Hanyoyi da Shawarwari

Addu’a
Cin jarabawa na bukatar hadin gwiwar ilimi, tsari, da kuma kyakkyawar niyya. A cikin wannan rubutun, zamu duba wasu sirrin da zasu taimaka wajen samun nasara a jarabawa.1. Tsara Lokaci ShiryawaKafa Tsarin Karatu: Yana da matukar Mahimmanci kayi amfani da kalandar ko agenda don tsara lokacin karatun ka. Ka tabbatar ka raba lokaci tsakanin darussa daban-daban. Sanya Jadawalin Jarabawa: Ka san lokacin jarrabawa da wuri, sannan ka tsara lokacin karatun ka bisa wannan Sanin. 2. Hanyoyin Koyo Karatu da Hujja: Yi Amfani da Koyarwa ta Hanya Mai Sauki: Yi amfani da hotuna, zane-zane, da takardun bayani don taimakawa wajen fahimta. Tsarin KaratuRaba Koyarwa: Kada ka yi karatu duka a lokaci guda. Raba darussa zuwa kashi-kashi, ka yi karatu a hankali. Yi Amfani da Lokacin Hutu: Ka...
Addu’ar Cin Jarrabawa (Exam): Muhimmancin Ta da Nasara

Addu’ar Cin Jarrabawa (Exam): Muhimmancin Ta da Nasara

Addu’a
A yau muna kawo muku Addu'ar wacce zakuyi A lokacin da wani Jarrabawa na Examination ko Gwaji makammancin haka ke tunkato ku, A lokacin jarrabawa, da damar dalibai na fuskantar damuwa, tsoro, da kuma rashin kwanciyar hankali. Wannan yanayi na iya haifar da tasiri mai kyau ko mara kyau ga sakamakon jarabawa. Saboda haka, yin addu'a na da matukar muhimmanci wajen samun nasara a jarrabawa. A cikin wannan rubutun, zamu tattauna kan yadda addu'a ke taimakawa, irin addu'o'in da za a iya yi, da kuma wasu shawarwari kan yadda za a tsarawa jarrabawa da kyau. Muhimmancin Addu'a a Lokacin Jarrabawa Addu'a wata hanya ce ta Neman Biyan bukata a gurin Allah. Yana ba mu damar bayyana bukatunmu da fatanmu, ko da kuwa suna da alaka da karatu ko rayuwa ta yau da kullum. Lokacin da muka yi addu'a, muna...
Warren Buffett: Mai Kuɗi na 7 a Duniya Ya ba da Tallafin Sama da Naira Tiriliyan 1.8

Warren Buffett: Mai Kuɗi na 7 a Duniya Ya ba da Tallafin Sama da Naira Tiriliyan 1.8

Duniya
Mai kudin duniya na bakwai, Warren Buffett, ya yi gagarumar kyautar kuɗi har dala biliyan 1.1 domin tallafawa al'umma a duniya. Wannan kyauta ta biyo bayan alkawarin da ya yi tun a shekarar 2006 na sadaukar da dukiyarsa don taimakon mutane. A ranar Litinin, Buffett, wanda ke da shekaru 94, ya sanar da rukunin kamfanin sa, Berkshire Hathaway, cewa ya bayar da kyautar makudan kudin. A halin yanzu, ana hasashen cewa rukunin kamfanin yana da kadara ta kimanin $1.1 trillion a fadin duniya. Kyautar ta kai ga cibiyoyin iyalansa kamar:- Cibiyar Susan Thompson Buffett- Cibiyar Sherwood- Cibiyar Howard G. Buffett- Cibiyar NoVo Buffett ya bayyana cewa yana son a raba sauran dukiyarsa ga 'ya'yansa uku da wani mutum da zai ambata daga baya idan rai ya yi halinsa. Wannan tunani ya biyo bayan ra...
Addu’ar Cin Jarabawa: Dogaro ga Allah a Lokacin Gwaji

Addu’ar Cin Jarabawa: Dogaro ga Allah a Lokacin Gwaji

Addu’a
A cikin rayuwar mu, lokaci-lokaci muna fuskantar ƙalubale da jarabawa. Wannan na iya zama daga cikin abubuwan da ke jawo damuwa, rashin tabbas, da kuma tashi hankali. A wannan lokaci ne ya kamata mu juya zuwa ga Allah, mai jujjuya zukata, tare da neman taimako da jagoranci. Addu'ar cin jarabawa na daga cikin hanyoyin da zamu iya amfani da su don neman taimakon Allah a cikin waɗannan lokuta. Menene Addu'ar Cin Jarabawa? Addu'ar cin jarabawa ita ce addu'ar da mutum ke yi don neman taimako daga Allah yayin da yake fuskantar jarabawa ko ƙalubale. Wannan addu'a na nufin neman karfin gwiwa, lafiya, da kuma jagoranci daga Allah domin shawo kan dukkanin matsaloli da ke gaban mu. اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْعَفْوَ وَالْعَافِيَةَ فِي الدُّنْيَا وَالْآخِرَةِ، اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ...
Yadda Ake Istikhara a Musulunci

Yadda Ake Istikhara a Musulunci

Addu’a
A yau zamu Yi muku bayani yadda Ake yin Istikhara a cikin musulunci, istikhara Wani adduar ne na Neman jagorancin a cikin al'amura. A Musulunci, ana yin istikhara lokacin da mutum ke da shakka ko kuma yana neman shawara kan wani abu mai muhimmanci. Ga yadda ake gudanar da istikhara: 1. Niyyah (Niyya)   - Ka fara da samun niyyar yin istikhara da zuciya. Ka sanar da Allah cewa kana neman shawararsa game da abin da kake son yi. 2. Yayin da ka tayar da Sallah inma na Farilla ko na Nafila bayan an Karan ta Suratul fatiha da ko Wani Sura da kake so sai ka karanta wannan adduar bayan hakanAn karbi daga Jaabir Ibn 'Abdullaah (Allah ya kara yarda da shi), ya ce: Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya kasance yana umurtar mu da yin addu’ar neman shiriya a cikin dukkan al’amura...
An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsakanin Isra’ila da Hezbollah

An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsakanin Isra’ila da Hezbollah

Duniya
Amurka ta sanar da cewa Isra'ila ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da mayakan Hezbollah da ke Kudancin Lebanon. Wannan yarjejeniyar ta biyo bayan shafe sama da shekara guda ana musayar wuta tsakanin dakarun Isra'ila da Hezbollah. Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bayyana cewa za a samu tsagaita wuta na tsawon watanni biyu, wanda zai ba da damar dakarun Isra'ila su janye daga Kudancin Lebanon, yayin da sojojin Lebanon za su mamaye wuraren da Hezbollah ke da iko. A martanin sa, shugaban Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce sojojinsa ba za su bata lokaci ba idan Hezbollah ta saɓa yarjejeniyar. Har yanzu, ba a ji daga kungiyar Hezbollah kan wannan yarjejeniyar ba, amma ba a sami wani alamar karya yarjejeniyar ba. Wakilin Amurka, Amos Hochstein, wanda ya jagoranci tattaunawar, ya bayyana...
Jam’iyyar PDP Ta Dakatar da Dan Majalisa, Ta Fadi Laifinsa<br>

Jam’iyyar PDP Ta Dakatar da Dan Majalisa, Ta Fadi Laifinsa

Siyasa
Jam'iyyar PDP a jihar Bauchi ta dakatar da ɗan majalisar dokokin jihar, Habibu Umar, mai wakiltar ƙaramar hukumar Kirfi. Wannan dakatarwar ta biyo bayan zargin rashin biyayya da aka yi masa. A cikin wasiƙar dakatarwar da jam'iyyar ta aike wa shugaban majalisar dokokin jihar, Abubakar Sulaiman, an bayyana cewa Habibu Umar ya sabawa sashe na 58 na kundin tsarin mulkin jam'iyyar na 2017. An kafa kwamitin ladabtarwa a ranar 11 ga watan Nuwamba, wanda ya gudanar da bincike kan zargin da ake masa. Bayan gudanar da bincike, kwamitin ya tabbatar da laifin da ake zarginsa, inda aka ba da shawarar dakatar da shi har sai an gudanar da taron hukunci. Daga ranar 25 ga watan Nuwamban 2024, an haramta masa shiga kowace harka da ta shafi jam'iyyar. Ana zargin Habibu Umar da ɗasawa da ministan bab...
Dakarun Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda da Dama Yayin Wani Artabu

Dakarun Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda da Dama Yayin Wani Artabu

Labarai
Dakarun sojojin rundunar hadin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) sun samu nasarar hallaka ƴan ta'adda a jihar Borno, inda aka kashe ƴan ta'adda 15 a lokacin wani samame da aka kai a garin Kukawa. A cikin sanarwa da rundunar MNJTF ta fitar, an bayyana cewa sojojin sun yi amfani da dabarun rubdugu ta sama da ƙasa a yankin Guzamala, wanda hakan ya haifar da raunuka ga ƴan ta'addan. Hakan na daga cikin nasarorin da aka samu wajen yaki da ƴan ta'addan ISWAP a yankin. Rundunar ta bayyana cewa sojojin sama sun gudanar da harin ne a kan ƴan ta'adda masu ɗauke da makamai da ke kan babura. A wannan samamen, dakarun sun hallaka ƴan ta'adda 15, yayin da aka kama ɗaya da rai. Haka zalika, an ƙwato makamai masu tarin yawa daga hannun ƴan ta'addan, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 guda bakwai, babb...
Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Ƙwararren Likita a Jihar Delta

Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Ƙwararren Likita a Jihar Delta

Labarai
Miyagun ƴan bindiga sun kai farmaki wani asibitin likita a jihar Delta, inda suka yi awon gaba da ƙwararren likita, Dr. Donatus Nwasor. Lamarin ya faru ne a daren ranar Talata, lokacin da likitan ke shirin tafiya gida. An ruwaito cewa maharan sun kutsa cikin asibitin da misalin ƙarfe 8:15 na dare. Wata majiya ta bayyana cewa likitan ya haɗa kayansa da nufin barin asibitin lokacin da ƴan bindigan suka farmake shi. A cewar majiyar, ƴan bindiga guda biyar ne suka fito daga daji, suka danne likitan suka tura shi cikin motarsa. Matar da ta shaida lamarin ta bayyana cewa, bayan an yi garkuwa da likitan, an gano motar sa a yashe a kusa da mahaɗar Iselegu. Hakan ya jawo damuwa a cikin al'umma, inda aka sanar da jami'an tsaro domin ɗaukar matakai na ceto likitan cikin ƙoshin lafiya. An san...
Ma’aikata Sun Yabawa Gwamnan Kano Bayan Dafe Sabon Albashi

Ma’aikata Sun Yabawa Gwamnan Kano Bayan Dafe Sabon Albashi

Labarai
Daga Kano, 27 Nuwamba , 2024 Kungiyoyin 'yan kwadago a jihar Kano sun bayyana gamsuwarsu da matakin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya dauka na biyan ma'aikata mafi karancin albashi. Wannan mataki na biyan sabbin albashi ya zo ne bayan gwamna Abba ya yi alkawarin inganta rayuwar ma'aikata a jihar.A cikin makonni uku da suka gabata, gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da cewa za a fara biyan ma'aikata mafi karancin albashi na N71,000, wanda ya wuce umarnin gwamnatin tarayya na biyan akalla N70,000. Wannan mataki ya jawo farin ciki a tsakanin ma'aikatan jihar, wanda suka yi alkawarin goyon bayan gwamnan saboda wannan kyakkyawan mataki.Kungiyar Kwadago ta kasa (NLC) a jihar Kano ta bayyana godiyarta ga gwamna Abba bisa wannan sabon mataki. Shugaban NLC na Kano, Kwamred Kabiru Inuwa, ya ce gyaran alba...