Rikicin Cikin Gida Ya yi Kamari a APC, An Kafa Kwamitin Sulhu
Jam’iyyar APC a jihar Adamawa ta kafa kwamitin sulhu mai mutum takwas domin daidaita rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyar. Wannan mataki ya biyo bayan taro da aka gudanar a Yola, wanda mataimakin shugaban APC na Arewa maso Gabas, Mustapha Salihu, ya jagoranta.A cikin sanarwar da sakataren yada labarai na APC a Adamawa, Mohammed Abdullahi, ya fitar, an bayyana cewa kwamitin na karkashin jagorancin Sanata Muhammed Mana. Kwamitin ya kunshi jiga-jigai kamar Sanatoci Bello Tukur, Abubakar Girei, Binta Garba, da Injiniya Martins Babale. Hakanan, Hon. Yusuf Buba Yakubu, Dr. Bridget Zidon, da Barista Isa Baba, wanda ke matsayin Sakataren kwamitin, sun hada da su.Aikin da aka dora wa kwamitin ya hada da warware matsalolin cikin gida da karfafa hadin kai tsakanin ’ya’yan jam’iyyar. Kwat...








