Addu’ar Neman Tsari Daga Sharrin Mutane

Assalamualaikum warahmatullahi wabarakatuhu, barkan mu da war haka, sannu ku da kasancewa tare da mu a Cikin wannan shafin namu a dai dai wannan lokacin


A cikin duniya mai cike da kalubale da sharruka daban daban, addu’a tana da matukar muhimmanci ga kowanne Musulmi. Addu’a tana bayar da kariya, da kuma taimaka mana wajen samun tsari daga sharrin mutane.

Rubutun mu zai yi nazari kan, addu’oin da ya kamata mu dinga Yi, da kuma mahimmancin sa da kuma hanyoyin da za mu iya amfani da ita wajen neman tsari daga sharrin mutane.

Mahimmancin Addu’a

Addu’a, tana matsayin ibada, tana da matukar daraja a cikin addinin Musulunci. Ta hanyar addu’a, muna bayyana bukatunmu ga Ubangiji Allahu SWT, muna neman taimako daga gare shi, da kuma neman kariya daga sharrin da zai iya zuwa daga mutane. Addu’a na iya zama hanya mai karfi wajen samun natsuwa da jin dadin, musamman a lokacin da muka fuskanci wahalhalu daga wasu.

Addu’o’in da za a yi

Akwai addu’o’in da aka koyar a cikin Alkur’ani da Hadisai wadanda zamu iya yi don samun tsari daga sharrin mutane. Wasu daga cikin su sun hada da:

1. Addu’ar Ayat al-Kursi: Wannan ayar tana bayar da kariya daga sharrin mutane da shaidan. Ana bada shawarar karanta ta bayan sallar farilla.

اللهُ لَا إِلَهَ إِلَّا هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ لَا تَأْخُذُهُ سِنَةٌ وَلَا نَوْمٌ لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ مَنْ ذَا الَّذِي يَشْفَعُ عِنْدَهُ إِلَّا بِإِذْنِهِ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَيْءٍ مِنْ عِلْمِهِ إِلَّا بِمَا شَاءَ وَسِعَ كُرْسِيُّهُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَلَا يَئُودُهُ حِفْظُهُمَا وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ

‎Allaahu laa ‘ilaaha ‘illaa Huwal-Hayyul-Qayyoom, laa ta’khuthuhu sinatun wa laa nawm, lahu maa fis-samaawaati wa maa fil-‘ardh, man thai-lathee yashfa’u ‘indahu ‘illaa bi’ithnih, ya’lamu maa bayna ‘aydeehim wa maa khalfahum, wa laa yuheetoona bishay’im-min ‘ilmihi ‘illaa bimaa shaa’a, wasi’a kursiyyuhus samaawaati wal’ardh, wa laa ya’ooduhu hifdhuhumaa, wa Huwal- ‘Aliyyul- ‘Adheem.

Allah! Babu abin bautawa bisa cancanta sai Shi, Rayayye, Mai rayawa, kuma Ya tsare dukkan abin da yake akwai. Barci ko gyangadi ba ya riske shi. Shi ne da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa. Wane ne wanda ke yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa? Ya san abin da zai same su a duniya, da abin da zai same su a Lahira. Kuma bã zã su kẽwayãwa da kõme ba daga ilminSa, fãce abin da Ya so. Al’arshinSa ya shimfiɗa sammai da ƙasa, kuma bã Ya jin gajiyar tsare su da tsare su. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma .


2. Addu’ar Falaq da Nas: Wannan surorin guda biyu ana kiran su Al-Mu’awwidhatayn tana nufin “masu karewa biyu” ko “surori biyu na neman tsari”  tana da matukar tasiri wajen neman tsari daga sharrin aljannu da mutane.

قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلْفَلَقِ, ‎مِن شَرِّ مَا خَلَقَ, ‎وَمِن شَرِّ غَاسِقٍ إِذَا وَقَبَ, ‎وَمِن شَرِّ ٱلنَّفَّـٰثَـٰتِ فِى ٱلْعُقَدِ, ‎وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
Ka ce: Ina nẽman tsari ga Ubangijin safiya
Daga sharrin abin da Ya halitta
Kuma daga sharrin dare idan yayi duhu
Kuma daga sharrin masu yin busa a kan ƙulle-ƙulle
‎Kuma daga sharrin mai hasada idan ya yi hasada.”

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ, ‎قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلنَّاس, ِ‎مَلِكِ ٱلنَّاسِ, ‎إِلَٰهِ ٱلنَّاس, ِ‎مِن شَرِّ ٱلْوَسْوَاسِ ٱلْخَنَّاس, ِ‎ٱلَّذِى يُوَسْوِسُ فِى صُدُورِ ٱلنَّاسِ, ‎مِنَ ٱلْجِنَّةِ وَٱلنَّاسِ

‎‎Bismillahir-Rahmanir-Raheem

‎Qul a’udhu birabbin-naas
Malikin-naas
‎Ilahin-naas
‎Min sharril-waswasil-khannaas
‎‎Allazhi yuwaswisu fi sudoorin-naas
‎Minal jinnati wan-naas

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai.

‎Ka ce: “Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne
Mammalakin mutane
‎Abun bautan mutane
Daga sharrin mai waswasi mai ja da baya
‎‎Wanda ke sanya waswasi a cikin zukatan mutane.
‎Daga aljannu da mutane.

‎3. Addu’ar ta uku

بِسْمِ الله الَّذِي لاَ يَضُرُّ مَعَ ا سْمِهِ شَيْئٌ فِي الأَ رْضِ وَ لاَ فِي السـَّماءِ وَ هُوَ السَّمِیعُ العَلِيمُ

Bismillāhi lla dhī lā yaḍurru ma‘a ismihi shay’un fil‑’ardi wa lā fis‑samā’i, wa huwa as‑samī‘u al‑‘alīm.

Da sunan Allah, wanda babu wani abu a cikin kasa ko sammai da ke cutar da suna sa, kuma Shi ne Mai ji, Masani.

Wannan addu’a tana bayar da kariya daga dukkan sharrin da dan Adam zai iya fuskanta.

Hanyoyin Amfani da Addu’a

1. Yin Addu’a da Zuciya Mai Tsabta

Yin addu’a tare da zuciya mai tsabta yana da matukar muhimmanci. Lokacin da muke yin addu’a, ya kamata mu mai da hankali ga kalmomin mu da hanyar da muke bayyana bukatunmu. Tsarkakiyar zuciya tana kara karfin addu’a.

2. Yin Addu’a a Lokaci Kafin Fuskantar Kalubale

Kafin mu fuskanci wani kalubale, yana da kyau mu yi addu’a. Misali, idan zamu tafi wani wuri ko mu hadu da wasu mutane wanda ba mu yarda da su ba, ko Kuma inda muka saba zuwa, Yana da mahimmacin muyi Addu’a don samun tsari da kariya.

3. Kula da Ibadar Sallah

Sallah tana da matukar muhimmanci a cikin rayuwar Musulmi. Ta hanyar yin sallah akai-akai, muna neman kusanci ga Allah, wanda yin hakan Zai zama kariya a gare mu daga dukkan sharrin da zamu iya fuskanta.

Kammalawa

Addu’a tana da matukar tasiri wajen neman tsari daga sharrin mutane. Ta hanyar yin addu’a da zuciya mai tsabta, muhimman addu’o’i, da kuma kula da ibada, zamu iya tabbatar da cewa Allah yana tare da mu a kowane lokaci. A karshe, ya kamata mu yi imani cewa Allah yana jin addu’armu, kuma yana bayar da kariya ga duk wanda ya nemi taimakonSa.

Muna fatan wannan rubutun ya taimaka wajen fahimtar damuwa daku gaba daya  mahimmancin addu’a da hanyoyin da za mu iya amfani da ita don samun tsari daga sharrin mutane.