Gwamnonin Najeriya Sun Nuna Alhini Kan Ambaliya a Neja



Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta bayyana damuwarta game da ambaliyar ruwa da ta faru a karamar hukumar Mokwa, jihar Neja, inda ta jefa rayukan mutane da yawa cikin hadari.

Shugaban NGF, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa wannan lamari ya tayar da hankali, yana mai nuna goyon baya ga gwamnati da al’ummar jihar Neja. Rahotanni sun tabbatar da cewa akalla mutane 21 sun rasa rayukansu, tare da asarar dukiya mai yawa.

AbdulRazaq ya ce, “Muna tare da gwamna Umaru Bago da al’ummar jihar Neja a wannan lokaci mai cike da kunci.” Kungiyar ta jaddada cewa ambaliyar ta zama babban al’amari da ke bukatar gaggawar daukar matakai na kariya.

Gwamnonin sun yaba wa matakan gaggawa da gwamnatin jihar Neja ta dauka tare da hukumomin agaji. Sun kuma yi kira ga jama’a da su goyi bayan dukkan matakan da gwamnati ke dauka don rage illar sauyin yanayi.

AbdulRazaq ya nemi addu’o’in al’umma domin samun sauki ga wadanda ambaliyar ta shafa, tare da rokon Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.